< Esias 3 >

1 Behold now, the Lord, the Lord of hosts, will take away from Jerusalem and from Judea the mighty man and mighty woman, the strength of bread, and the strength of water,
Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
2 the great and mighty man, the warrior and the judge, and the prophet, and the counsellor, and the elder,
jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
3 the captain of fifty also, and the honorable counsellor, and the wise artificer, and the intelligent hearer.
shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
4 And I will make youths their princes, and mockers shall have dominion over them.
“Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
5 And the people shall fall, man upon man, and [every] man upon his neighbor: the child shall insult the elder man, and the base the honorable.
Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
6 For a man shall lay hold of his brother, as one of his father's household, saying, You have raiment, be you our ruler, and let my meat be under you.
Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
7 And he shall answer in that day, and say, I will not be your ruler; for I have no bread in my house, nor raiment: I will not be the ruler of this people.
Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
8 For Jerusalem is ruined, and Judea has fallen, and their tongues [have spoken] with iniquity, disobedient [as they are] towards the Lord.
Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
9 Therefore now their glory has been brought low, and the shame of their countenance has withstood them, and they have proclaimed their sin as Sodom, and made it manifest.
Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
10 Woe to their soul, for they have devised an evil counsel against themselves, saying against themselves, Let us bind the just, for he is burdensome to us: therefore shall they eat the fruits of their works.
Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
11 Woe to the transgressor! evils shall happen to him according to the works of his hands.
Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
12 O my people, your exactors strip you, and extortioners rule over you: O my people, they that pronounce you blesses lead you astray, and pervert the path of your feet.
Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
13 But now the Lord will stand up for judgment, and will enter into judgment with his people.
Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
14 The Lord himself shall enter into judgment with the elders of the people, and with their rulers: but why have you set my vineyard on fire, and [why is] the spoil of the poor in your houses?
Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
15 Why do you wrong my people, and shame the face of the poor?
Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
16 Thus says the Lord, Because the daughters of Sion are haughty, and have walked with an outstretched neck, and with winking of the eyes, and motion of the feet, at the same time drawing their garments in trains, and at the same time sporting with their feet:
Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
17 therefore the Lord will humble the chief daughters of Sion, and the Lord will expose their form in that day;
Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
18 and the Lord will take away the glory of their raiment, the curls and the fringes, and the crescents,
A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
19 and the chains, and the ornaments of their faces,
’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
20 and the array of glorious ornaments, and the armlets, and the bracelets, and the wreathed work, and the finger-rings, and the ornaments for the right hand,
kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
21 and the ear-rings, and the garments with scarlet borders, and the garments with purple grounds, and the shawls to be worn in the house, and the Spartan transparent dresses, and those made of fine linen, and the purple [ones], and the scarlet [ones], and the fine linen, interwoven with gold and purple, and the light coverings for couches.
da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
22 And there shall be instead of a sweet smell, dust; and instead of a girdle, you shall gird yourself with a rope; and instead of a golden ornament for the head, you shall have baldness on account of your works; and instead of a tunic with a scarlet ground, you shall gird yourself with sackcloth.
tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
23 And your most beautiful son whom you love shall fall by the sword; and your mighty men shall fall by the sword, and shall be brought low.
da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
24 And the stores of your ornaments shall mourn, and you shall be left alone, and shall be levelled with the ground.
A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.

< Esias 3 >