< Osee 7 >
1 When I have healed Israel, then shall the iniquity of Ephraim be revealed, and the wickedness of Samaria; for they have wrought falsehood: and a thief shall come in to him, [even] a robber spoiling in his way;
a duka sa’ad da zan warkar da Isra’ila, zunuban Efraim za su tonu za a kuma bayyana laifofin Samariya. Suna ruɗu, ɓarayi sukan fasa su shiga gidaje,’yan fashi sukan yi fashi a tituna;
2 that they may concert together as [men] singing in their heart: I remember all their wickedness: now have their own counsels compassed them about; they came before my face.
amma ba su gane cewa na tuna da dukan ayyukan muguntarsu ba. Zunubansu sun kewaye su; kullum suna a gabana.
3 They gladdened kings with their wickedness, and princes with their lies.
“Suna faranta wa sarki zuciya da muguntarsu, shugabanni kuma da ƙarairayinsu.
4 They are all adulterers, as an oven glowing with flame for hot-baking, on account of the kneading of the dough, until it is leavened.
Dukansu mazinata ne suna ƙuna kamar matoya wadda mai gashin burodi ba ya bukata yă tura mata wuta daga cuɗe kullu har kumburinsa.
5 [In] the days of our kings, the princes began to be inflamed with wine: he stretched out his hand with pestilent fellows.
A ranar bikin sarkinmu shugabanni sukan bugu da ruwan inabi, yă yi cuɗanya da masu ba’a.
6 Therefore their hearts are inflamed as an oven, while they rage all the night: Ephraim is satisfied with sleep; the morning is come; he is burnt up as a flame of fire.
Zukatansu suna kamar matoya; sukan kusace shi da wayo. Muguwar aniyarsu takan yi ta ci dukan dare; da safe sai ta ƙuna kamar harshen wuta.
7 They are all heated like an oven, and have devoured their judges: all their kings are fallen; there was not among them one that called on me.
Dukansu suna da zafi kamar matoya; suna kashe masu mulkinsu. Dukan sarakunansu sukan fāɗi, kuma babu waninsu da yake kira gare ni.
8 Ephraim is mixed among his people; Ephraim became a cake not turned.
“Efraim yana cuɗanya da al’ummai; Efraim waina ne mai fāɗi da ba a juye ba.
9 Strangers devoured his strength, and he knew [it] not; and grey hairs came upon him, and he knew [it] not.
Baƙi sun tsotse ƙarfinsa, amma bai gane ba. Gashi kansa ya cika da furfura, amma bai lura ba.
10 And the pride of Israel shall be brought down before his face: yet they have not returned to the Lord their God, neither have they diligently sought him for all this.
Girmankan Isra’ila ya ba da shaida a kansa, amma duk da haka bai dawo ga Ubangiji Allahnsa ko yă neme shi ba.
11 And Ephraim was as a silly dove, not having a heart: he called to Egypt, and they went to the Assyrians.
“Efraim yana kama da kurciya, marar wayo, marar hankali, yanzu yana kira ga Masar, yanzu yana juyewa ga Assuriya.
12 Whenever they shall go, I will cast my net upon them; I will bring them down as the birds of the sky, I will chasten them with the rumor of their [coming] affliction.
Sa’ad da suka tafi, zan jefa ragata a kansu; zai janye su ƙasa kamar tsuntsayen sararin sama. Sa’ad da na ji suna tafiya tare, zan kama su.
13 Woe to them! for they have started aside from me: they are cowards; for they have sinned against me: yet I redeemed them, but they spoke falsehoods against me.
Kaitonsu, domin sun kauce daga gare ni! Hallaka za tă aukar musu, domin sun tayar mini! Na ƙudura in cece su amma suna faɗar ƙarya a kaina.
14 And their hearts did not cry to me, but they howled on their beds: they pined for oil and wine.
Ba sa yin mini kuka da zuciyarsu amma suna ihu a kan gadajensu. Sukan taru wurin ɗaya don hatsi da ruwan inabi amma su juya mini baya.
15 They were instructed by me, and I strengthened their arms; and they devised evils against me.
Na horar da su na kuma ƙarfafa su, amma sun ƙulla mini maƙarƙashiya.
16 They turned aside to that which is not, they became as a bent bow: their princes shall fall by the sword, by reason of the unbridled state of their tongue: this is their setting at nothing in the land of Egypt.
Ba sa juya ga Mafi Ɗaukaka; suna kama da tanƙwararren baka. Za a kashe shugabanninsu da takobi saboda banzan maganganunsu. Saboda wannan za a wulaƙanta su a ƙasar Masar.