< Osee 11 >

1 Early in the morning were they cast off, the king of Israel has been cast off: for Israel is a child, and I loved him, and out of Egypt have I called his children.
“Sa’ad da Isra’ila yake yaro, na ƙaunace shi, daga Masar kuma na kira ɗana.
2 As I called them, so they departed from my presence: they sacrificed to Baalim, and burnt incense to graven images.
Amma yawan kiran da na yi wa Isra’ila haka nesa da ni da suke ta yi. Suka miƙa hadaya ga Ba’al suka kuma ƙona turare ga siffofi.
3 Yet I bound the feet of Ephraim, I took him on my arm; but they knew not that I healed them.
Ni ne na koya wa Efraim tafiya ina kama su da hannu; amma ba su gane cewa ni ne na warkar da su ba.
4 When men were destroyed, I drew them with the bands of my love: and I will be to them as a man striking [another] on his cheek: and I will have respect to him, I will prevail with him.
Na bishe su da linzamin alheri da tausayi, da ragamar ƙauna; Na cire karkiya daga wuyansu na kuma rusuna na ciyar da su.
5 Ephraim lived in Egypt; and [as for] the Assyrian, he was his king, because he would not return.
“Ba za su koma Masar ba Assuriya kuma ba za tă yi mulki a bisansu ba saboda sun ƙi su tuba ba?
6 And in his cities he prevailed not with the sword, and he ceased [to war] with his hands: and they shall eat [of the fruit] of their own devices:
Takuba za su yi ta wulgawa a biranensu, za su hallaka sandunan ƙarafan ƙofofinsu su kuma kawo ƙarshen ƙulle-ƙullensu.
7 and his people [shall] cleave fondly to their habitation; but God shall be angry with his precious things, and shall not at all exalt him.
Mutanena sun ƙudura su juye daga gare ni. Ko da ma suka yi kira ga Mafi Ɗaukaka, ta ko ƙaƙa ba zai girmama su ba.
8 How shall I deal with you, Ephraim? [how] shall I protect you, Israel? what shall I do with you? I will make you as Adama, and as Seboim; my heart is turned at once, my repentance is powerfully excited.
“Yaya zan ba da kai, Efraim? Yaya zan miƙa ka, Isra’ila? Yaya zan yi da kai kamar Adma? Yaya zan yi da kai kamar Zeboyim? Zuciyata ta canja a cikina; dukan tausayina ya huru.
9 I will not act according to the fury of my wrath, I will not abandon Ephraim to be utterly destroyed: for I am God, and not man; the Holy One within you: and I will not enter into the city.
Ba zan zartar da fushina mai zafi ba, ba kuwa zan juya in ragargaza Efraim ba. Gama ni Allah ne, ba mutum ba, Mai Tsarki a cikinku. Ba zan zo cikin fushi ba.
10 I will go after the Lord: he shall utter [his voice] as a lion: for he shall roar, and the children of the waters shall be amazed.
Za su bi Ubangiji; zai yi ruri kamar zaki. Sa’ad da ya yi ruri,’ya’yansa za su zo da rawan jiki daga yamma.
11 They shall be amazed [and fly] as a bird out of Egypt, and as a dove out of the land of the Assyrians: and I will restore them to their houses, says the Lord.
Za su zo da rawan jiki kamar tsuntsaye daga Masar, kamar kurciyoyi daga Assuriya. Zan zaunar da su a cikin gidajensu,” in ji Ubangiji.
12 Ephraim has compassed me with falsehood, and the house of Israel and Juda with ungodliness: [but] now God knows them, and they shall be called God's holy people.
Mutanen Efraim sun kewaye ni da ƙarairayi, gidan Isra’ila da ruɗu. Mutanen Yahuda kuma suna yi wa Allah ƙin ji, har ma a kan Mai Tsarkin nan mai aminci.

< Osee 11 >