< Osee 10 >

1 Israel is a vine with goodly branches, her fruit is abundant: according to the multitude of her fruits she has multiplied [her] altars; according to the wealth of his land, he has set up pillars.
Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
2 They have divided their hearts; now shall they be utterly destroyed: he shall dig down their altars, their pillars shall mourn.
Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
3 Because now they shall say, We have no king, because we feared not the Lord:
Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
4 and what should a king do for us, speaking false professions [as his] words? he will make a covenant: judgment shall spring up as a weed on the soil of the field.
Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
5 The inhabitants of Samaria shall dwell near the calf of the house of On; for the people of it mourned for it: and as they provoked him, they shall rejoice at his glory, because he has departed from them.
Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
6 And having bound it for the Assyrians, they carried it away as presents to king Jarim: Ephraim shall receive a gift, and Israel shall be ashamed of his counsel.
Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
7 Samaria has cast off her king as a twig on the surface of the water.
Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
8 And the altars of On, the sins of Israel, shall be taken away: thorns and thistles shall come up on their altars; and they shall say to the mountains, Cover us; and to the hills, Fall on us.
Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
9 From the time the hills [existed] Israel has sinned: there they stood: war [waged] against the children of iniquity
“Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
10 to chastise them shall not overtake them on the hill, the nations shall be gathered against them, when they are chastened for their two sins,
Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
11 Ephraim is a heifer taught to love victory, but I will come upon the fair part of her neck: I will mount Ephraim; I will pass over Juda in silence; Jacob shall prevail against him.
Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
12 Sow to yourselves for righteousness, gather in for the fruit of life: light you for yourselves the light of knowledge; seek the Lord till the fruits of righteousness come upon you.
Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
13 Therefore have you passed over ungodliness in silence, and reaped the sins of it? you have eaten false fruit; for you has trusted in your sins, in the abundance of your power.
Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
14 Therefore shall destruction rise up among your people, and all your strong places shall be ruined: as a prince Solomon [departed] out of the house of Jeroboam, in the days of battle they dashed the mother to the ground upon the children,
hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
15 thus will I do to you, O house of Israel, because of the unrighteousness of your sins.
Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.

< Osee 10 >