< Jezekiel 5 >

1 And you, son of man, take you a sword sharper than a barber's razor; you shall procure it for yourself, and shall bring it upon your head, and upon your beard: and you shall take a pair of scales, and shall separate the hair.
“Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki takobi mai kaifi ka kuma yi amfani da shi kamar rezan mai aski don askin kanka da gemunka. Sa’an nan ka ɗauki ma’auni ka kuma raba gashin.
2 A fourth part you shall burn in the fire in the midst of the city, at the fulfillment of the days of the siege: and you shall take a fourth part, and burn it up in the midst of it: and a fourth part you shall cut with a sword round about it: and a fourth part you shall scatter to the wind; and I will draw out a sword after them.
Sa’ad da kwanakin ƙawanyarka sun ƙare, sai ka ƙone kashi ɗaya bisa uku na gashin da wuta a cikin birnin. Ka ɗauki kashi ɗaya bisa uku ka yayyanka shi da takobi kewaye da birnin. Ka kuma watsar da kashi ɗaya bisa uku a iska. Gama zan fafare su da takobin da aka zāre.
3 And you shall take thence a few in number, and shall wrap them in the fold of your garment.
Amma ka ɗibi gashi kaɗan ka daure a shafin rigarka.
4 And you shall take of these again, and cast them into the midst of the fire, and burn them up with fire: from thence shall come forth fire; and you shall say to the whole house of Israel,
Har yanzu, ka ɗibi kaɗan na waɗannan ka zuba su cikin wuta su kuma ƙone. Wuta zai bazu daga nan zuwa dukan gidan Isra’ila.
5 Thus says the Lord; This is Jerusalem: I have set her and the countries round about her in the midst of the nations.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Urushalima ce wannan, wadda na kafa a tsakiyar al’ummai, da ƙasashe kewaye da ita a ko’ina.
6 And you shall declare mine ordinances to the lawless one from out of the nations; and my statutes [to the sinful one] of the countries round about her: because they have rejected mine ordinances, and have not walked in my statutes.
Duk da haka cikin muguntarta ta yi tayarwa a kan dokokina da ƙa’idodina fiye da al’ummai da ƙasashe kewaye da ita. Ta ƙi dokokina ba tă kuwa bi ƙa’idodina ba.
7 Therefore thus says the Lord, Because your occasion [for sin has been taken] from the nations round about you, and you have not walked in my statutes, nor kept mine ordinances, nay, you have not even done according to the ordinances of the nations round about you; therefore thus says the Lord;
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce kin yi ƙin ji fiye da al’umman da suke kewaye da ke ba ki kuma bi ƙa’idodina ko ki kiyaye dokokina ba. Ba ki ma dace da matsayin al’umman da suke kewaye da ke ba.
8 Behold, I am against you, and I will execute judgment in the midst of you in the sight of the nations.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Ni kaina ina gāba da ke, Urushalima, kuma zan hukunta ki a gaban al’ummai.
9 And I will do in you things which I have not done, and the like of which I will not do again, for all your abominations.
Saboda dukan gumakan banƙyamarki, zan yi abin da ban taɓa yi ba, ba kuwa zan ƙara yinsa ba.
10 Therefore the fathers shall eat [their] children in the midst of you, and children shall eat [their] fathers; and I will execute judgments in you, and I will scatter all that are left of you to every wind.
Saboda haka a cikinki ubanni za su ci’ya’yansu,’ya’ya kuma za su ci ubanninsu. Zan hukunta ki zan kuma watsar da dukan waɗanda suke tsira da suke naki a iska.
11 Therefore, [as] I live, says the Lord; surely, because you have defiled my holy things with all your abominations, I also will reject you; mine eye shall not spare, and I will have no mercy.
Saboda haka muddin ina a raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin kin ƙazantar da wuri mai tsarkina da dukan mugayen siffofinki da kuma ayyukanki masu banƙyama, ni kaina zan janye alherina; ba zan ji tausayinki ko in haƙura da ke ba.
12 A fourth part of you shall be cut off by pestilence, and a fourth part of you shall be consumed in the midst of you with famine: and [as for another] fourth part of you, I will scatter them to every wind; and a fourth part of you shall fall by sword round about you, and I will draw out a sword after them.
Kashi ɗaya bisa uku na mutanenki za su mutu da annoba ko su mutu da yunwa a cikinki; kashi ɗaya bisa uku takobi ne zai kashe su a waje da katangarki; kashi ɗaya bisa uku kuma zan watsar a iska in kuma fafare su da takobin da aka zāre.
13 And my wrath and mine anger shall be accomplished upon them: and you shall know that I the Lord have spoken in my jealousy, when I have accomplished mine anger upon them.
“Sa’an nan ne fushina zai huce hasalata a kanki kuma ta lafa, in kuma wartsake. Kuma sa’ad da na zuba fushina a kansu, a sa’an nan ne za su san cewa Ni Ubangiji na yi magana a cikin fushin kishina a kansu.
14 And I will make you desolate, and your daughters round about you, in the sight of every one that passes through.
“Zan mai da ki kufai da kuma abin dariya a cikin al’ummai kewaye da ke, a gaban dukan waɗanda suke wucewa.
15 And you shall be mourned over and miserable among the nations round about you, when I have executed judgments in you in the vengeance of my wrath. I the Lord have spoken.
Za ki zama abin dariya da abin ba’a, kashedi da abin banrazana ga al’ummai kewaye da ke sa’ad da na hukunta ki cikin fushi da cikin hasala da kuma tsawatawa mai zafi. Ni Ubangiji na faɗa.
16 And when I have sent against them shafts of famine, then they shall be consumed, and I will break the strength of your bread.
Sa’ad da na harbe ki da mugayen kibiyoyina da kuma kibiyoyi masu hallakarwa na yunwa, zan yi harbi don in kashe ki. Zan kawo ƙarin yunwa a kanki in kuma yanke tanadin abincinki.
17 So I will send forth against you famine and evil beasts, and I will take vengeance upon you; and pestilence and blood shall pass through upon you; and I will bring a sword upon you round about. I the Lord have spoken.
Zan aika da yunwa da namun jeji a kanki, za su kuma bar ku ba’ya’ya. Annoba da zub da jini za su ratsa cikinki, zan kuma kawo takobi a kanki. Ni Ubangiji na faɗa.”

< Jezekiel 5 >