< Jezekiel 4 >
1 And you, son of man, take you a brick, and you shall set it before your face, and shall portray on it the city, [even] Jerusalem.
“Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki tubalin yumɓu, ka ajiye shi a gabanka ka kuma zāna birnin Urushalima a kansa.
2 And you shall besiege it, and build works against it, and throw up a mound round about it, and pitch camps against it, and set up engines round about.
Sa’an nan ka yi mata ƙawanya. Ka kafa mata katangar ƙawanya, ka gina katangar da ɗan tudu ka kewaye ta da dundurusai.
3 And take you to yourself an iron pan, and you shall set it [for] an iron wall between you and the city: and you shall set your face against it, and it shall be in a siege, and you shall besiege it. This is a sign to the children of Israel.
Sa’an nan ka ɗauki kwanon ƙarfe, ka shirya shi kamar katangar ƙarfe tsakaninka da birnin ka kuma zuba mata ido. Za tă kasance a ƙarƙashin ƙawanya, kai kuwa za ka yi mata ƙawanya. Wannan zai zama alama ga gidan Isra’ila.
4 And you shall lie upon your left side, and lay the iniquities of the house of Israel upon it, according to the number of the hundred and fifty days [during] which you shall lie upon it: and you shall bear their iniquities.
“Sa’an nan ka kwanta a hagunka ka kuma sa zunubin gidan Isra’ila a kanka. Za ka ɗauki zunubinsu na waɗansu kwanakin da kake kwance a gefenka.
5 For I have appointed you their iniquities for a number of days, for a hundred and ninety days: so you shall bear the iniquities of the house of Israel.
Na ɗora maka kwanaki bisa ga shekarun zunubinsu. Saboda haka cikin kwana 390 za ka ɗauki zunubin gidan Isra’ila.
6 And you shall accomplish this, and [then] shall lie on your right side, and shall bear the iniquities of the house of Juda forty days: I have appointed you a day for a year.
“Bayan ka gama haka, ka sāke kwantawa, a wannan lokaci a gefen damarka, ka kuma ɗauki zunubin gidan Yahuda. Na ɗora maka kwanaki 40, kwana guda a madadin shekara guda.
7 So you shall set your face to the siege of Jerusalem, and shall strengthen your arm, and shall prophesy against it.
Ka juya fuskarka wajen ƙawanyar Urushalima da hannunka a buɗe ka yi annabci a kanta.
8 And, behold, I have prepared bonds for you, land you may not turn from your one side to the other, until the days of your siege shall be accomplished.
Zan ɗaura ka da igiyoyi don kada ka juya daga wannan gefe zuwa wani gefe sai ka gama kwanakin ƙawanyarka.
9 Take you also to you wheat, and barley, and beans, and lentils, and millet, and bread-corn; and you shall cast them into one earthen vessel, and shall make them into loaves for yourself; and you shall eat them a hundred and ninety days, according to the number of the days [during] which you sleep on your side.
“Ka ɗauki alkama da sha’ir, wake da acca, gero da maiwa; ka sa su a tulun ajiya ka kuma yi amfani da su don yin burodi wa kanka. Za ka ci shi a kwanaki 390 da za ka kwanta a gefenka.
10 And you shall eat your food by weight, twenty shekels a day: from time to time shall you eat them.
Ka auna shekel ashirin na abinci don kowace rana ka kuma ci shi a ƙayyadadden lokaci.
11 And you shall drink water by measure, even from time to time you shall drink the sixth part of a hin.
Haka ma ka auna kashi ɗaya bisa shida na garwan ruwa ka sha shi a ƙayyadadden lokaci.
12 And you shall eat them [as] a barley cake: you shall bake them before their eyes in man's dung.
Ka ci abinci yadda za ka ci ƙosai sha’ir, ka gasa shi a gaban mutane, ka yi amfani da najasar mutane kamar itacen wuta.”
13 And you shall say, Thus says the Lord God of Israel; Thus shall the children of Israel eat unclean things among the Gentiles.
Ubangiji ya ce, “Ta haka mutanen Isra’ila za su ci ƙazantaccen abinci a cikin al’ummai inda zan kore su in kai.”
14 Then I said, Not so, Lord God of Israel: surely my soul has not been defiled with uncleanness; nor have I eaten, that which died of itself or was torn of beasts from my birth until now; neither has any corrupt flesh entered into my mouth.
Sai na ce, “Ba haka ba ne, Ubangiji Mai Iko Duka! Ban taɓa ƙazantar da kaina ba. Daga ƙuruciyata har zuwa yanzu ban taɓa cin wani abin da aka samu ya mutu ko abin da namun jeji suka kashe ba. Ba nama marar tsabtan da ya taɓa shiga bakina.”
15 And he said to me, Behold, I have given you dung of oxen instead of man's dung, and you shall prepare your loaves upon it.
Sai ya ce, “To da kyau, zan bari ka gasa burodin a kan kashin shanu a maimakon najasar mutane.”
16 And he said to me, Son of man, behold, I break the support of bread in Jerusalem: and they shall eat bread by weight and in lack; and shall drink water by measure, and in a state of ruin:
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, zan yanke tanadin abinci a Urushalima. Mutane za su auna abincin da za su ci da tsoro su kuma auna ruwan da za su sha cikin fargaba,
17 that they may lack bread and water; and a man and his brother shall be brought to ruin, and they shall pine away in their iniquities.
domin abinci da ruwa za su kāsa. Za su damu da ganin juna za su kuma lalace saboda zunubinsu.