< Jezekiel 18 >

1 And the word of the Lord came to me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Son of man, what mean you by this parable among the children of Israel, saying, The fathers have eaten unripe grapes, and the children's teeth have been set on edge?
“Me ku mutane kuke nufi da faɗar wannan karin magana a kan ƙasar Isra’ila cewa, “‘Ubanni sun ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya kuwa sun mutu’?
3 [As] I live, says the Lord, surely this parable shall no more be spoken in Israel.
“Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba za ku ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.
4 For all souls are mine; as the soul of the father, so also the soul of the son, they are mine: the soul that sins, it shall die.
Gama kowane mai rai nawa ne, mahaifi da ɗa, duk nawa ne. Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu.
5 But the man who shall be just, who executes judgment and righteousness,
“A ce akwai mai adalci wanda yake aikata abin da yake daidai da kuma gaskiya;
6 who shall not eat upon the mountains, and shall not at all lift up his eyes to the devices of the house of Israel, and shall not defile his neighbor's wife, and shall not draw near to her that is removed,
ba ya cin abinci a duwatsun tsafi ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Ba ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa ko ya kwana da mace lokacin al’adarta ba.
7 and shall not oppress any man, [but] shall return the pledge of the debtor, and shall be guilty of no plunder, shall give his bread to the hungry, and clothe the naked;
Ba ya cin zalin wani, amma yakan mayar wa wanda ya ba shi jingina abin da ya jinginar masa. Ba ya yi fashi amma yakan ba wa mayunwata abinci ya kuma tanada wa marasa tufafi riga.
8 and shall not lend his money upon usury, and shall not receive usurious increase, and shall turn back his hand from injustice, shall execute righteous judgment between a man and his neighbor,
Ba ya ba da bashi da ruwa ko ya karɓa ƙarin riba. Yakan janye hannunsa daga aikata mugunta yakan kuma yi shari’a cikin gaskiya tsakanin mutum da mutum.
9 and has walked in my commandments and kept mine ordinances, to do them; he is righteous, he shall surely live, says the Lord.
Yana bin ƙa’idodina yana kuma kiyaye dokokina da aminci. Wannan mutumin adali ne; tabbatacce zai rayu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
10 And if he beget a mischievous son, shedding blood and committing sins,
“A ce yana da ɗa wanda yana kisa ko yana yin ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa
11 who has not walked in the way of his righteous father, but has even eaten upon the mountains, and has defiled his neighbor's wife,
(ko da yake mahaifin bai yi ko ɗaya daga cikinsu ba). “Yakan ci abinci a duwatsun tsafi. Yakan ƙazantar da matar maƙwabci.
12 and has oppressed the poor and needy, and has committed robbery, and not restored a pledge, and has set his eyes upon idols, has wrought iniquities,
Yakan ci zalin matalauta da mabukata. Yakan yi fashi. Ba ya mayar da abin da aka jinginar masa. Ya dogara ga gumaka. Yana aikata ayyukan banƙyama.
13 has lent upon usury, and taken usurious increase; he shall by no means live: he has wrought all these iniquities; he shall surely die; his blood shall be upon him.
Yakan ba da bashi da ruwa ya kuma karɓi riba mai yawa. Irin wannan mutum zai rayu? Ba zai rayu ba! Domin ya aikata dukan waɗannan abubuwa masu banƙyama, tabbatacce za a kashe shi, kuma hakkin jininsa zai zauna a kansa.
14 And if he beget a son, and [the son] see all his father's sins which he has wrought, and fear, and not do according to them,
“Amma a ce wannan ɗa yana da ɗa wanda ya ga dukan zunuban da mahaifinsa yake aikata, kuma ko da yake ya gan su, bai yi ko ɗaya daga cikin irin abubuwan nan ba, wato,
15 and [if he] has not eaten on the mountains, and has not set his eyes on the devices of the house of Israel, and has not defiled his neighbor's wife,
“Bai ci abinci a duwatsun tsafi ba ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Bai ƙazantar da matar maƙwabcinsa ba.
16 and has not oppressed a man, and has not retained the pledge, nor committed robbery, has given his bread to the hungry, and has clothed the naked,
Bai ci zalin wani ko ya karɓi jingina ba. Ba ya fashi amma yakan ba da abincinsa ga mayunwata ya tanada tufafi wa marasa tufafi.
17 and has turned back his hand from unrighteousness, has not received interest or usurious increase, has wrought righteousness, and walked in mine ordinances; he shall not die for the iniquities of his father, he shall surely live.
Yakan janye hannunsa daga zunubi ba ya kuma ba da bashi da ruwa ko karɓan riba da yawa. Yakan kiyaye dokokina ya kuma bi ƙa’idodina. Ba zai mutu saboda zunubin mahaifinsa ba; tabbatacce zai rayu.
18 But if his father grievously afflict, or plunder, he has wrought enmity in the midst of my people, and shall die in his iniquity.
Amma mahaifinsa zai mutu saboda zunubinsa, domin ya yi ƙwace, ya yi wa ɗan’uwansa fashi ya kuma yi abin da ba daidai ba a cikin mutanensa.
19 But you will say, Why has not the son borne the iniquity of the father? Because the son has wrought judgment and mercy, has kept all my statues, and done them, he shall surely live.
“Duk da haka kukan yi tambaya, ‘Me ya sa ɗan ba zai sami rabo a laifin mahaifinsa ba?’ Da yake ɗan ya yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina, tabbatacce zai rayu.
20 But the soul that sins shall die: and the son shall not bear the iniquity of the father, nor shall the father bear the iniquity of the son: the righteousness of the righteous shall be upon him, and the iniquity of the transgressor shall be upon him.
Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu. Ɗa ba zai sami rabo a laifin mahaifi ba, mahaifi ba zai sami rabo a laifi ɗa ba. Adalcin adali zai zama nasa, muguntar mugu za tă koma kansa.
21 And if the transgressor turn away from all his iniquities which he has committed, and keep all my commandments, and do justice and mercy, he shall surely live, and shall by no means die.
“Amma in mugun mutum ya juya daga dukan zunubin da ya aikata ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina ya kuwa yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
22 None of his trespasses which he has committed shall be remembers: in his righteousness which he has done he shall live.
Babu laifin da ya yi da za a tuna da su. Saboda abubuwan adalcin da ya aikata, zai rayu.
23 Shall I at all desire death of the sinner, says the Lord, as I [desire] that he should turn from [his] evil way, and live?
Ina jin daɗin mutuwar mugu ne? In ji Ubangiji Mai Iko Duka. A maimako, ban fi jin daɗi sa’ad da suka juyo daga hanyoyinsu suka rayu ba?
24 But when the righteous man turns away from his righteousness, and commits iniquity, according to all the transgressions which the transgressor has wrought, none of his righteousness which he has wrought shall be at all remembered: in his trespass wherein he has trespassed, and in his sins wherein he has sinned, in them shall he die.
“Amma in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya yi zunubi ya kuma aikata abubuwa masu banƙyamar da mugun mutum ke aikatawa, zai rayu? Babu abubuwan adalcin da ya aikata da za a tuna da su. Saboda rashin amincinsa da kuma saboda zunubai da ya yi, zai mutu.
25 Yet you have said, The way of the Lord is not straight. Hear now, all the house of Israel; will not my way be straight? Is your way straight?
“Duk da haka kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ka ji, ya gidan Isra’ila. Hanyata ba daidai ba ce?
26 When the righteous turns away from his righteousness and commits a trespass, and dies in the trespass he has committed, he shall [even] die in it.
In mai adalci ya juye daga adalcinsa ya yi zunubi, zai mutu saboda wannan; saboda zunubin da ya yi, zai mutu.
27 And when the wicked man turns away from his wickedness that he has committed, and shall do judgment and justice, he has kept his soul,
Amma in mugun mutum ya juye daga muguntarsa ya kuma yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, zai ceci ransa.
28 and has turned away from all his ungodliness which he has committed: he shall surely live, he shall not die.
Domin ya lura da dukan laifofin da ya yi ya kuma juye daga gare su, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
29 Yet the house of Israel say, The way of the Lord is not right. Is not my way right, O house of Israel? is not your way wrong?
Duk da haka mutanen Isra’ila sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Hanyoyina ba daidai ba ne, ya gidan Isra’ila? Ba hanyoyinku ne ba daidai ba?
30 I will judge you, O house of Israel, says the Lord, each one according to his way: be converted, and turn from all your ungodliness, and it shall not become to you the punishment of iniquity.
“Saboda haka, ya gidan Isra’ila, zan hukunta ku, kowa bisa ga hanyarsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba! Ku juye daga dukan laifofinku; sa’an nan zunubi ba zai zama sanadin fāɗuwarku ba.
31 Cast away from yourselves all your ungodliness wherein you have sinned against me; and make to yourselves a new heart and a new spirit: for why should you die, O house of Israel?
Ku raba kanku da dukan laifofin da kuka yi, ku sami sabuwar zuciya da sabon ruhu. Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?
32 For I desire not the death of him that dies, says the Lord.
Gama ba na jin daɗin mutuwar wani, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba don ku rayu!

< Jezekiel 18 >