< Exodus 5 >

1 And after this went in Moses and Aaron to Pharao, and they said to him, These things says the Lord God of Israel, Send my people away, that they may keep a feast to me in the wilderness.
Daga bisani sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Bari mutanena su tafi domin su yi mini biki a hamada.’”
2 And Pharao said, Who is he that I should listen to his voice, so that I should send away the children of Israel? I do not know the Lord, and I will not let Israel go.
Fir’auna ya ce, “Wane ne Ubangiji da zan yi biyayya da shi, har in bar Isra’ila su tafi? Ban san Ubangiji ba, kuma ba zan bar Isra’ila su tafi ba.”
3 And they say to him, The God of the Hebrews has called us to him: we will go therefore a three days' journey into the wilderness, that we may sacrifice to the Lord our God, lest at any time death or slaughter happen to us.
Sai suka ce, “Allah na Ibraniyawa ya sadu da mu. Yanzu bari mu ɗauki tafiyar kwana uku cikin hamada domin mu miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnmu, don kada yă buga mu da annoba ko takobi.”
4 And the king of Egypt said to them, Why do you, Moses and Aaron, turn the people from their works? depart each of you to your works.
Amma sarkin Masar ya ce wa, “Musa da Haruna, don me kuke hana mutane yin aikinsu? Ku koma wurin aikinku!”
5 And Pharao said, Behold now, the people is very numerous; let us not then give them rest from their work.
Sa’an nan Fir’auna ya ce, “Ga shi mutane sun yi yawa a ƙasar Masar, ku kuma yanzu kuna so ku hana su yin aiki.”
6 And Pharao gave orders to the taskmasters of the people and the accountants, saying,
A wannan rana Fir’auna ya ba da wannan umarni wa shugabannin masu gandu,
7 You shall no longer give straw to the people for brick-making as yesterday and the third day; but let them go themselves, and collect straw for themselves.
“Kada ku ƙara ba wa mutanen ciyawar tattaka domin su yi tubula, bari su tafi su tattara tattaka da kansu.
8 And you shall impose on them daily the rate of brick-making which they perform: you shall not abate anything, for they are idle; therefore have they cried, saying, Let us arise and do sacrifice to our God.
Ku kuma bukace su su yi tubula daidai yawan tubalin da suka saba yi, kada ku rage. Ragwaye ne, shi ya sa suke kuka cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya ga Allahnmu.’
9 Let the works of these men be made grievous, and let them care for these things, and not care for vain words.
Ku sa waɗannan mutane su yi aiki mai tsanani sosai, don kada su sami zarafin kasa kunne ga maganganun ƙarya.”
10 And the taskmasters and the accountants hastened them, and they spoke to the people, saying, thus says Pharao, I [will] give you straw no longer.
Sai shugabannin masu aikin gandu suka fita suka gaya wa mutanen Isra’ila, “Ga abin da Fir’auna ya ce, ‘Ba zan ƙara ba ku tattaka ba.
11 Go you, yourselves, get for yourselves straw whenever you can find it, for nothing is diminished from your rate.
Ku tafi ku nemo wa kanku tattaka duk inda za ku samu, amma ba za a rage aikinku ba ko kaɗan.’”
12 So the people were dispersed in all the land of Egypt, to gather stubble for straw.
Saboda haka mutane suka warwatsu ko’ina a Masar domin tattara bunnun da za su yi amfani da su, maimakon tattaka.
13 and the taskmasters hastened them, saying, Fulfil your regular daily tasks, even as when straw was given you.
Shugabannin gandu suka dinga matsa musu suna cewa, “Ku cika aikin da aka bukace ku na kowace rana kamar yadda kuke yi sa’ad da kuke da tattaka.”
14 And the accountants of the race of the children of Israel, who were set over them by the masters of Pharao, were scourged, [[and questioned, ] men] saying, Why have you not fulfilled your rates of brick work as yesterday and the third day, today also?
Manyan Isra’ilawa waɗanda shugabannin gandun Fir’auna suka naɗa, suka sha dūka, aka kuma yi musu tambayoyi ana cewa, “Don me ba ku cika yawan tubula na jiya da na yau kamar yadda kuka saba ba?”
15 And the accountants of the children of Israel went in and cried to Pharao, saying, Why do you act thus to your servants?
Sai manyan Isra’ila masu bi da aikin gandu suka tafi wurin Fir’auna suka yi roƙo suna cewa, “Don me kake yi wa bayinka haka?
16 Straw is not given to your servants, and they tell us to make brick; and behold your servants have been scourged: you will therefore injure your people.
Ba a ba wa bayinka tattaka, duk da haka ana ce mana, ‘Ku yi tubula!’ Ana wa bayinka dūka, amma fa laifin na mutanenka ne.”
17 And he said to them, You are idle, you are idlers: therefore you say, Let us go [and] do sacrifice to our God.
Fir’auna ya ce, “Ku ragwaye ne! Shi ya sa kuke cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya wa Ubangiji.’
18 Now then go and work, for straw shall not be given to you, yet you shall return the rate of bricks.
Ku ɓace yanzu daga nan, ku koma wurin aikinku. Ba za a ba ku tattaka ba, kuma dole ku fid da tubula kamar yadda kuka saba.”
19 And the accountants of the children of Israel saw themselves in an evil plight, [men] saying, You shall not fail to deliver the daily rate of the brick-making.
Manyan Isra’ilawa da suke bi da aikin gandu suka gane cewa sun shiga uku, sa’ad da aka gaya musu, “Ba za ku rage yawan tubulan da aka bukace ku ku yi na kowace rana ba.”
20 And they met Moses and Aaron coming forth to meet them, as they came forth from Pharao.
Da suka bar Fir’auna, sai suka sadu da Musa da Haruna suna jira su sadu da su,
21 And they said to them, The Lord look upon you and judge you, for you have made our savor abominable before Pharao, and before his servants, to put a sword into his hands to kill us.
sai suka ce, “Bari Ubangiji yă duba, yă kuma hukunta ku! Kun maishe mu abin ƙyama ga Fir’auna da bayinsa, kuka kuma sa musu takobi a hannunsu don su kashe mu.”
22 And Moses turned to the Lord, and said, I pray, Lord, why have you afflicted this people? and therefore have you sent me?
Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, don me ka kawo wahala a kan mutanen nan? Abin da ya sa ka aiko ni ke nan?
23 For from the time that I went to Pharao to speak in your name, he has afflicted this people, and you have not delivered your people.
Gama tun da na tafi wurin Fir’auna, na yi masa magana da sunanka, sai ya fara gasa wa mutanen nan azaba, ba ka kuma ceci mutanenka.”

< Exodus 5 >