< Exodus 17 >

1 And all the congregation of the children of Israel departed from the wilderness of Sin, according to their encampments, by the word of the Lord; and they encamped in Raphidin: and there was no water for the people to drink.
Dukan taron Isra’ilawa suka kama tafiya daga Hamadar Sin, suka yi ta tafiya suna sauka a wurare dabam-dabam bisa ga umarnin Ubangiji. A ƙarshe suka sauka a Refidim, suka zauna a can, amma ba ruwan da jama’a za su sha.
2 And the people reviled Moses, saying, Give us water, that we may drink; and Moses said to them, Why do you revile me, and why tempt you the Lord?
Saboda haka suka yi wa Musa maganganun banza suka ce, “Ba mu ruwa mu sha.” Musa ya amsa ya ce, “Don me kuke mini maganganun banza? Don me kuke gwada Ubangiji?”
3 And the people thirsted there for water, and there the people murmured against Moses, saying, Why is this? have you brought us up out of Egypt to kill us and our children and our cattle with thirst?
Amma mutanen suka yi fama da ƙishirwa a can, suka yi gunaguni a kan Musa. Suka ce, “Don me ka fitar da mu daga Masar, ka sa mu da’ya’yanmu da dabbobinmu, mu mutu da ƙishirwa?”
4 And Moses cried to the Lord, saying, What shall I do to this people? yet a little while and they will stone me.
Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Me zan yi da wannan jama’a? Suna shiri su jajjefe ni da duwatsu.”
5 And the Lord said to Moses, Go before this people, and take to yourself of the elders of the people; and the rod with which you struck the river, take in your hand, and you shall go.
Ubangiji amsa wa Musa, “Ka ɗauki sandan da ka bugi ruwan Nilu da shi. Ka kira waɗansu shugabannin Isra’ila, ku wuce a gaban jama’ar.
6 Behold, I stand there before you [come], on the rock in Choreb, and you shall strike the rock, and water shall come out from it, and the people shall drink. And Moses did so before the sons of Israel.
Zan tsaya a can a gabanka, kusa da dutsen Horeb. Ka bugi dutsen, ruwa kuwa zai fito daga gare shi domin mutane su sha.” Sai Musa ya yi haka a idon dattawan Isra’ila.
7 And he called the name of that place, Temptation, and Reviling, because of the reviling of the children of Israel, and because they tempted the Lord, saying, Is the Lord among us or not?
Sai suka ba wa wurin suna, Massa da Meriba, saboda Isra’ilawa sun yi jayayya, suka kuma gwada Ubangiji cewa, “Ubangiji yana tsakaninmu ko babu?”
8 And Amalec came and fought with Israel in Raphidin.
Amalekawa suka zo, suka yaƙi Isra’ilawa a Refidim.
9 And Moses said to Joshua, Choose out for yourself mighty men, and go forth and set the army in array against Amalec to-morrow; and, behold, I [shall] stand on the top of the hill, and the rod of God [will be] in my hand.
Musa ya ce wa Yoshuwa, “Zaɓi waɗansu mazanmu, ka je ka yaƙi Amalekawa. Gobe zan tsaya a bisa tudu, da sandan Allah a hannuwana.”
10 And Joshua did as Moses said to him, and he went out and set the army in array against Amalec, and Moses and Aaron and Or went up to the top of the hill.
Sai Yoshuwa ya yaƙi Amalekawa kamar yadda Musa ya umarta, Musa, Haruna da Hur kuwa suka tafi bisa tudu.
11 And it came to pass, when Moses lifted up his hands, Israel prevailed; and when he let down his hands, Amalec prevailed.
Muddin hannun Musa yana a miƙe, sai Isra’ilawa su yi ta cin nasara, amma da zarar hannunsa ya sauka, sai Amalekawa su yi ta cin nasara.
12 But the hands of Moses were heavy, and they took a stone and put it under him, and he sat upon it; and Aaron and Or supported his hands one on this side and the other on that, and the hands of Moses were supported till the going down of the sun.
Sa’ad da hannuwan Musa suka gaji, sai Haruna da Hur suka ɗauki dutse suka sa ya zauna a kai. Sa’an nan su kuma suka tsaya gefe da gefe, suna riƙe da hannuwansa har fāɗuwar rana.
13 And Joshua routed Amalec and all his people with the slaughter of the sword.
Sai Yoshuwa kuwa ya ci nasara a kan Amalekawa da takobi.
14 And the Lord said to Moses, Write this for a memorial in a book, and speak [this] in the ears of Joshua; for I will utterly blot out the memorial of Amalec from under heaven.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka rubuta wannan a cikin littafi, yă zama abin tuni, ka kuma faɗa wa Yoshuwa zan hallaka Amalekawa ƙaƙaf daga duniya.”
15 And Moses built an altar to the Lord, and called the name of it, The Lord my Refuge.
Musa ya gina bagade, sai ya kira shi Ubangiji shi ne Tutata.
16 For with a secret hand the Lord wages war upon Amalec to all generations.
Ya ce, “Gama an ɗaga hannuwa sama zuwa kursiyin Ubangiji, Ubangiji zai yaƙi Amalekawa daga tsara zuwa tsara.”

< Exodus 17 >