< Deuteronomy 5 >

1 And Moses called all Israel, and said to them, Hear, Israel, the ordinances and judgments, all that I speak in your ears this day, and you shall learn them, and observe to do them.
Musa ya tattara dukan Isra’ila ya ce, Ku ji, ya Isra’ila, ƙa’idodi da dokokin da na furta a kunnuwanku a yau. Ku koye su, ku kuma tabbata kun bi su.
2 The Lord your God made a covenant with you in Choreb.
Ubangiji Allahnmu ya yi alkawari da mu a Horeb.
3 The Lord did not make this covenant with your fathers, but with you: you are all here alive this day.
Ba da kakanninmu ba ne Ubangiji ya yi wannan alkawari, amma da mu ne, da dukanmu waɗanda muke da rai a yau.
4 The Lord spoke to you face to face in the mountain out of the midst of the fire.
Ubangiji ya yi magana fuska da fuska da ku daga wuta a kan dutse.
5 And I stood between the Lord and you at that time to report to you the words of the Lord, (because you were afraid before the fire, and you went not up to the mountain) saying,
(A wannan lokaci na tsaya tsakanin Ubangiji da ku, don in furta muku maganar Ubangiji, domin kun ji tsoron wutar, ba ku kuwa hau dutsen ba.) Ya ce,
6 I am the Lord your God, who brought you out of the land of Egypt, out of the house of bondage.
“Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
7 You shall have no other gods before my face.
“Ba za ka kasance da waɗansu alloli a gabana ba.
8 You shall not make to yourself an image, nor likeness of any thing, whatever things [are] in the heaven above, and whatever [are] in the earth beneath, and whatever [are] in the waters under the earth.
Ba za ka yi wa kanka gunki, ko wata siffar abin da take a sama a bisa, ko siffar abin da yake a duniya a ƙasa, ko siffar abin da yake a cikin ruwa a ƙarƙashin ƙasa ba.
9 You shall not bow down to them, nor shall you serve them; for I am the Lord your God, a jealous God, visiting the sins of the fathers upon the children to the third and fourth generation to them that hate me,
Ba za ka rusuna musu, ko ka yi musu sujada ba. Gama Ni, Ubangiji Allahnka, Allah ne mai kishi, nakan hukunta’ya’ya saboda zunuban iyaye har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suka ƙi ni.
10 and doing mercifully to thousands of them that love me, and that keep my commandments.
Amma nakan nuna ƙauna ga dubban tsararraki na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye dokokina.
11 You shall not take the name of the Lord your God in vain, for the Lord your God will certainly not acquit him that takes his name in vain.
Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai ba wa duk mai yin amfani da sunansa a banza laifi.
12 Keep the sabbath day to sanctify it, as the Lord your God commanded you.
Ka kiyaye ranar Asabbaci ta wurin kiyaye ta da tsarki, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka.
13 Six days you shall work, and you shall do all your works;
Kwanaki shida za ka yi aiki, ka kuma yi dukan aikinka,
14 but on the seventh day [is] the sabbath of the Lord your God: you shall do in it no work, you, and your son, and your daughter, your man-servant, and your maidservant, your ox, and your ass, and all your cattle, and the stranger that sojourns in the midst of you; that your man-servant may rest, and your maid, and your ox, as well as you.
amma rana ta bakwai, Asabbaci ne ga Ubangiji Allahnka. A kanta ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawanka, ko baiwarka, ko saniyarka, ko jakinka, ko wani daga dabbobinka, ko baƙo a ƙofofinka, don bayinka maza da mata su ma su huta, kamar ka.
15 And you shall remember that you were a slave in the land of Egypt, and the Lord your God brought you out thence with a mighty hand, and a high arm: therefore the Lord appointed you to keep the sabbath day and to sanctify it.
Ka tuna fa, dā kai bawa ne a ƙasar Masar amma Ubangiji Allahnka ya fitar da kai daga can da iko da kuma ƙarfi. Saboda haka Ubangiji Allahnka ya umarce ka ka kiyaye ranar Asabbaci.
16 Honor your father and your mother, as the Lord your God commanded you; that it may be well with you, and that you may live long upon the land, which the Lord your God gives you.
Ka ba da girma ga mahaifinka da mahaifiyarka, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka, don ka yi tsawon rai, ka kuma sami zaman lafiya a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
17 You shall not commit murder.
Kada ka yi kisankai.
18 You shall not commit adultery.
Kada ka yi zina.
19 You shall not steal.
Kada ka yi sata.
20 You shall not bear false witness against your neighbor.
Kada ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka.
21 You shall not covet your neighbor's wife; you shall not covet your neighbor's house, nor his field, nor his man-servant, nor his maid, nor his ox, nor his ass, nor any beast of his, nor any thing that is your neighbor's.
Kada ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka. Kada kuma ka yi sha’awar gidan maƙwabcinka, ko gonarsa, ko bayinsa maza da mata, ko saniyarka, ko jakinsa, ko dai wani abin da yake na maƙwabtanka.”
22 These words the Lord spoke to all the assembly of you in the mountain out of the midst of the fire—[there was] darkness, blackness, storm, a loud voice—and he added no more, and he wrote them on two tables of stone, and he gave them to me.
Waɗannan su ne dokokin da Ubangiji ya furta da babbar murya ga taronku gaba ɗaya, a can dutse ta tsakiyar wuta, girgije da kuma baƙin duhu; bai kuma ƙara kome ba. Sa’an nan ya rubuta su a kan alluna biyu na dutse, ya kuma ba ni su.
23 And it came to pass when you heard the voice out of the midst of the fire, for the mountain burned with fire, that you came to me, even all the heads of your tribes, and your elders:
Sa’ad da kuka ji muryar daga duhu, yayinda dutsen yana cin wuta, dukan manyan kabilanku da dattawanku suka zo wurina.
24 and you said, Behold, the Lord our God has shown us his glory, and we have heard his voice out of the midst of the fire: this day we have seen that God shall speak to man, and he shall live.
Kuka kuma ce, “Ubangiji Allahnmu ya nuna mana ɗaukakarsa da zatinsa, mun kuma ji muryarsa a tsakiyar wutar. A yau mun ga cewa mutum zai iya rayu idan ma Allah ya yi magana da shi.
25 And now let us not die, for this great fire will consume us, if we shall hear the voice of the Lord our God any more, and we shall die.
Amma yanzu, don me za mu mutu? Wannan wuta mai girma za tă cinye mu, za mu kuwa mutu in muka ci gaba da jin muryar Ubangiji Allahnmu.
26 For what flesh [is there] which has heard the voice of the living God, speaking out of the midst of the fire, as we [have heard], and shall live?
Gama wanda ɗan adam ne ya taɓa jin muryar Allah mai rai yana magana daga wuta, kamar yadda muka ji, ya kuma tsira?
27 Do you draw near, and hear all that the Lord our God shall say, and you shall speak to us all things whatever the Lord our God shall speak to you, and we will hear, and do.
Kai, ka matsa kusa, ka saurara ga dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa. Sa’an nan ka faɗa mana dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa maka. Za mu saurara, mu kuma yi biyayya.”
28 And the Lord heard the voice of your words as you spoke to me; and the Lord said to me, I have heard the voice of the words of this people, even all things that they have said to you. [They have] well [said] all that they have spoken.
Ubangiji ya ji ku, sa’ad da kuka yi magana da ni, sai Ubangiji ya ce mini, “Na ji abin da wannan mutane suka faɗa maka. Abin da suka faɗa daidai ne.
29 O that there were such a heart in them, that they should fear me and keep my commands always, that it might be well with them and with their sons for ever.
Kash, da a ce zukatansu za su zama masu tsorona, su kuma kiyaye dukan dokokina kullum mana, saboda kome yă zama da lafiya gare su, da kuma’ya’yansu har abada!
30 Go, say to them, Return you to your houses;
“Je, ka faɗa musu su koma tentunansu.
31 but stand you here with me, and I will tell you all the commands, and the ordinances, and the judgments, which you shall teach them, and let them do so in the land which I give them for an inheritance.
Kai kuwa ka tsaya a nan tare da ni saboda in ba ka umarnai, ƙa’idodi da kuma dokoki duka, da za ka koya musu don su bi a ƙasar da nake ba su, su mallaka.”
32 And you shall take heed to do as the Lord your God commanded you; you shall not turn aside to the right hand or to the left,
Sai ku yi hankali don ku yi abin da Ubangiji Allahnku ya umarce ku; kada ku juya dama ko hagu.
33 according to all the way which the Lord your God commanded you to walk in it, that he may give you rest; and that it may be well with you, and you may prolong your days on the land which you shall inherit.
Ku yi tafiya cikin dukan hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, saboda ku zauna, ku yi nasara, ku kuma yi tsawon rai a ƙasar da za ku mallaka.

< Deuteronomy 5 >