< Deuteronomy 26 >

1 And it shall be when you shall have entered into the land, which the Lord your God gives you to inherit it, and you shall have inherited it, and you shall have lived upon it,
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta,
2 that you shall take of the first of the fruits of your land, which the Lord your God gives you, and you shall put them into a basket, and you shall go to the place which the Lord your God shall choose to have his name called there.
sai ku ɗauki’ya’yan fari na dukan amfanin gonar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku zuba a kwando. Sa’an nan ku je wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă zama mazauni don Sunansa,
3 And you shall come to the priest who shall be in those days, and you shall say to him, I testify this day to the Lord my God, that I am come into the land which the Lord sware to our fathers to give to us.
ku faɗa wa firist da yake aiki a lokacin, “Na sakankance yau ga Ubangiji Allahnka, cewa na zo ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninmu.”
4 And the priest shall take the basket out of your hands, and shall set it before the altar of the Lord your God:
Firist ɗin zai karɓi kwandon daga hannuwanku yă sa shi a ƙasa a gaban bagaden Ubangiji Allahnku.
5 and he shall answer and say before the Lord your God, My father abandoned Syria, and went down into Egypt, and sojourned there with a small number, and became there a mighty nation and a great multitude.
Sa’an nan za ku furta a gaban Ubangiji Allahnku cewa, “Mahaifina mutumin Aram ne mai yawo, ya gangara zuwa Masar da mutane kaɗan, ya zauna a can, ya kuma zama babban al’umma, mai iko da kuma mai yawa.
6 And the Egyptians afflicted us, and humbled us, and imposed hard tasks on us:
Amma Masarawa suka wulaƙanta mu suka sa muka sha wahala, suna sa mu aikin dole.
7 and we cried to the Lord our God, and the Lord heard our voice, and saw our humiliation, and our labor, and our affliction.
Sai muka yi kuka ga Ubangiji Allahn kakanninmu, Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya kuma azabar da muke sha, da wahalar da muke sha, da danniyar da suke yin mana.
8 And the Lord brought us out of Egypt himself with his great strength, and his mighty hand, and his high arm, and with great visions, and with signs, and with wonders.
Sai Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu mai ƙarfi da kuma iko, da razana mai girma da kuma alamu banmamaki da al’ajabai.
9 And he brought us into this place, and gave us this land, a land flowing with milk and honey.
Ya kawo mu wannan wuri, ya kuma ba mu wannan ƙasa, ƙasa mai zub da madara da kuma zuma;
10 And now, behold, I have brought the first of the fruits of the land, which you gave me, O Lord, a land flowing with milk and honey: and you shall leave it before the Lord your God, and you shall worship before the Lord your God;
yanzu kuwa na kawo’ya’yan fari na gonar da kai, ya Ubangiji ka ba ni.” Sai ku sa kwandon a gaban Ubangiji Allahnku, sa’an nan ku rusuna a gabansa.
11 and you shall rejoice in all the good [things], which the Lord your God has given you, [you] and your family, and the Levite, and the stranger that is within you.
Ku da Lawiyawa da baƙin da suke a cikinku, za ku yi murna cikin dukan abubuwa masu kyau da Ubangiji Allahnku ya ba ku tare da gidanku.
12 And when you shall have completed all the tithings of your fruits in the third year, you shall give the second tenth to the Levite, and stranger, and fatherless, and widow; and they shall eat it in your cities, and be merry.
Sa’ad da kuka gama fitar da kashi ɗaya bisa goma na dukan amfanin gona a shekara ta uku, shekarar zakka, za ku ba da su ga Balawe, baƙo, maraya da kuma gwauruwa, don su ci a cikin garuruwanku su ƙoshi.
13 And you shall say before the Lord your God, I have fully collected the holy things out of my house, and I have given them to the Levite, and the stranger, and the orphan, and the widow, according to all commands which you did command me: I did not transgress your command, and I did not forget it.
Sa’an nan ku faɗa wa Ubangiji Allahnku, “Na cire tsattsarkan rabo daga gidana na kuma ba wa Balawe, baƙo, maraya da gwauruwa, bisa ga dukan abin da ka umarta. Ban ja gefe daga umarnanka ko in manta da wani a cikinsu ba.
14 And in my distress I did not eat of them, I have not gathered of them for an unclean purpose, I have not given of them to the dead; I have listened to the voice of the Lord our God, I have done as you have commanded me.
Ban ci wani daga cikin tsattsarkan rabo yayinda nake makoki, ko in cire wani rabo mai tsarki yayinda nake marar tsarki, ko in miƙa wani sashensa ga matattu ba. Na yi biyayya ga Ubangiji Allahna, na aikata kome da ka umarce ni.
15 Look down from your holy house, from heaven, and bless your people Israel, and the land which you have given them, as you did swear to our fathers, to give to us a land flowing with milk and honey.
Ka duba ƙasa daga sama, mazauninka mai tsarki, ka albarkace mutanenka Isra’ila da kuma ƙasar da ka ba mu kamar yadda ka yi wa kakanninmu alkawari da rantsuwa, ƙasa mai zub da madara da zuma.”
16 On this day the Lord your God charged you to keep all the ordinances and judgments; and you shall observe and do them, with all your heart, and with all your soul.
Yau Ubangiji Allahnku ya umarce ku ku bi waɗannan ƙa’idodi da kuma dokoki, cikin natsuwa ku kiyaye su da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
17 You have chosen God this day to be your God, and to walk in all his ways, and to observe his ordinances and judgments, and to listen to his voice.
Kun furta a wannan rana cewa Ubangiji shi ne Allahnku, cewa za ku kuma yi tafiya a hanyoyinsa, cewa za ku kiyaye ƙa’idodinsa, umarnansa da kuma dokokinsa, kuka kuma ce za ku yi masa biyayya.
18 And the Lord has chosen you this day that you should be to him a peculiar people, as he said, to keep his commands;
Ubangiji kuwa ya furta a wannan rana cewa ku mutanensa ne, mallakarsa kamar yadda ya yi alkawari, da kuma cewa za ku kiyaye dukan umarnansa.
19 and that you should be above all nations, as he has made you renowned, and a boast, and glorious, that you should be a holy people to the Lord your God, as he has spoken.
Ya furta cewa zai sa ku zama masu yabo, masu suna, masu daraja, fiye da dukan al’umman da ya yi. Za ku zama jama’a tsattsarka ta Ubangiji Allahnku, kamar yadda ya yi alkawari.

< Deuteronomy 26 >