< Daniel 5 >

1 Baltasar the king made a great supper for his thousand nobles, and [there was] wine before the thousand.
Sarki Belshazar ya yi babban biki domin dubban hakimansa ya kuma sha ruwan inabi tare da su.
2 And Baltasar drinking gave orders as he tasted the wine that they should bring the gold and silver vessels, which Nabuchodonosor his father had brought forth from the temple in Jerusalem; that the king, and his nobles, and his mistresses, and his concubines, should drink out of them.
Yayinda Belshazar yake shan ruwan inabi, sai ya umarta a kawo zinariya da azurfan da Nebukadnezzar mahaifinsa ya kwaso daga haikali a Urushalima, saboda sarki da hakimansa, da matansa da ƙwarƙwaransa su sha da su.
3 So the gold and silver vessels were brought which [Nabuchodonosor] had taken out of the temple of God in Jerusalem; and the king, and his nobles, and his mistresses, and his concubines, drank out of them.
Sai suka kawo kayan zinariyan nan da aka kwaso daga haikalin Allah a Urushalima, sarki kuwa da hakimansa, da matansa, da ƙwarƙwaransa suka yi ta sha da su.
4 They drank wine, and praised the gods of gold, and of silver, and of brass, and of iron, and of wood, and of stone.
Yayinda suke shan ruwan inabin, sai suka yabi allolin zinariya da azurfa, da na tagulla, da na ƙarfe, da na itace da kuma na dutse.
5 In the same hour came forth fingers of a man's hand, and wrote in front of the lamp on the plaster of the wall of the king's house: and the king saw the knuckles of the hand that wrote.
Nan da nan sai ga yatsotsin hannun mutum sun bayyana, suna yin rubutu a kan shafen bangon, kusa da wurin da ake ajiye fitilar fadar sarki. Sarki kuwa yana ganin hannun yayinda yake rubutu.
6 Then the king's countenance changed, and his thoughts troubled him, and the joints of his loins were loosed, and his knees struck one another.
Sai fuskarsa ta ruɗe, ya kuma ji tsoro ƙwarai har gwiwoyinsa suka yi ta bugun juna, ƙafafunsa kuma suka rasa ƙarfi.
7 And the king cried aloud to bring in the magicians, Chaldeans, [and] soothsayers; and he said to the wise men of Babylon, Whosoever shall read this writing, and make known to me the interpretation, shall be clothed with scarlet, and [there shall be] a golden chain upon his neck, and he shall be the third ruler in my kingdom.
Sai sarki ya kira masu dabo, masanan taurari da masu duba, a kawo su, ya kuma ce wa masu hikima na Babilon, “Duk wanda ya karanta wannan rubutu ya kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa, zai zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
8 Then came in all the king's wise men: but they could not read the writing, nor make known the interpretation to the king.
Sa’an nan sai dukan masu hikima suka zo ciki, amma ba su iya karanta rubutun ba ko su faɗa wa sarki abin da yake nufi.
9 And king Baltasar was troubled, and his countenance changed upon him, and his nobles were troubled with him.
Saboda haka Sarki Belshazar ya firgita ƙwarai kuma fuskarsa ta ƙara ruɗewa. Hakimansa kuma suka rikice.
10 Then the queen came into the banquet house, and said, O king, live for ever: let not your thoughts trouble you, and let not your countenance be changed.
Sai sarauniya, da jin muryoyi na sarki da na hakimansa, ta shiga babban ɗakin liyafar. Ta ce, “Ya sarki, ranka yă daɗe! Kada ka firgita! Kada fuskarka ta ruɗe!
11 There is a man in your kingdom, in whom is the Spirit of God; and in the days of your father watchfulness and understanding were found in him; and king Nabuchodonosor your father made him chief of the enchanters, magicians, Chaldeans, [and] soothsayers.
Akwai wani mutum a masarautarka wanda yake da ruhun alloli masu tsarki a cikinsa. A zamanin mahaifinka an gane cewa yana da basira da hazaka da hikima kamar na alloli. Sarki Nebukadnezzar mahaifinka, mahaifinka sarki, na ce, ya naɗa shugaban masu dabo, da masu sihiri, masanan taurari da kuma masu duba.
12 For [there is] an excellent spirit in him, and sense and understanding in him, interpreting dreams [as he does], and answering hard [questions], and solving difficulties: [it is] Daniel, and the king gave him the name of Baltasar: now then let him be called, and he shall tell you the interpretation of the writing.
Wannan mutum Daniyel, wanda sarki ya kira Belteshazar, an gane yana da ruhu nagari, da ilimi, da ganewa don yin fassarar mafarkai, da bayyana ma’anar kacici-kacici, da warware al’amura masu wuya. Ka kira Daniyel shi kuwa zai faɗa maka abin da rubutun nan yake nufi.”
13 Then Daniel was brought in before the king: and the king said to Daniel, Are you Daniel, of the children of the captivity of Judea, which the king my father brought?
Saboda haka aka kawo Daniyel a gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Kai ne Daniyel ɗin nan, ɗaya daga cikin kamammu waɗanda mahaifina sarki ya kawo daga Yahuda?
14 I have heard concerning you, that the Spirit of God is in you, and [that] watchfulness and understanding and excellent wisdom have been found in you.
Na sami labari cewa kana da ruhun alloli a cikinka da kuma basira, da hazaka da kuma fitacciyar hikima.
15 And now, the wise men, magicians, [and] soothsayers, have come in before me, to read the writing, and make known to me the interpretation: but they could not tell it me.
An kawo masu hikima da masu dabo a gabana domin su karanta wannan rubutu su kuma faɗa mini abin da yake nufi, amma ba su iya ba.
16 And I have heard concerning you, that you are able to make interpretations: now then if you shall be able to read the writing, and to make known to me the interpretation of it, you shall be clothed with purple, and there shall be a golden chain upon your neck, and you shall be third ruler in my kingdom.
Na sami labari cewa kana iya ba da fassara da kuma warware matsaloli masu wuya. In har ka iya karanta wannan rubutun ka kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa maka riga shunayya, a kuma sa sarƙar zinariya a wuyanka. Za ka zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
17 And Daniel said, before the king, Let your gifts be to yourself, and give the present of your house to another; but I will read the writing, and will make known to you the interpretation of it.
Sai Daniyel ya amsa wa sarki ya ce, “Za ka iya ajiye kyautar wa kanka ko kuma ka ba wa wani. Duk da haka, zan karanta wa sarki rubutun, in kuma faɗa abin da yake nufi.
18 O king, the most high God gave to your father Nabuchodonosor a kingdom, and majesty, and honor, and glory:
“Ya sarki, Allah Mafi Ɗaukaka ya ba mahaifinka Nebukadnezzar sarauta, da girma, da ɗaukaka, da martaba.
19 and by reason of the majesty which he gave to him, all nations, tribes, [and] languages trembled and feared before him: whom he would he killed; and whom he would he struck; and whom he would he exalted; and whom he would he abased.
Saboda irin matsayin da ya ba shi, dukan mutane da al’ummai da kuma dukan harsuna suka ji tsoronsa suka yi rawar jiki a gabansa. Bisa ga ganin damarsa yakan kashe wani, ya bar wani da rai, haka kuma yakan ɗaukaka wani, ya ƙasƙantar da wani.
20 But when his heart was lifted up, and his spirit was emboldened to act proudly, he was deposed from his royal throne, and [his] honor was taken from him.
Amma da lokacin da zuciyarsa ta cika da girman kai ta kuma taurare, sai aka kore shi daga gadon sarautarsa, aka raba shi kuma da darajarsa.
21 And he was driven forth from men; and his heart was given him after the nature of wild beasts, and his dwelling was with the wild asses; and they fed him with grass as an ox, and his body was bathed with the dew of heaven; until he knew that the most high God is Lord of the kingdom of men, and will give it to whoever he shall please.
Aka kore shi daga cikin mutane aka kuma ba shi tunani irin na dabba; ya yi zama tare da jakunan jeji, ya kuma ci ciyawa kamar shanu; jikinsa kuma ya jiƙe da raɓa, har zuwa lokacin da ya gane, ashe, Allah Maɗaukaki ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
22 And you accordingly, his son, O Baltasar, has not humbled your heart before God: know you not all this?
“Amma kai ɗansa, Ya Belshazar, ba ka ƙasƙantar da kanka ba, ko da yake ka san wannan duka.
23 And you has been exalted against the Lord God of heaven; and they have brought before you the vessels of his house, and you, and your nobles, and your mistresses, and your concubines, have drunk wine out of them; and you has praised the gods of gold, and silver, and brass, and iron, and wood, and stone, which see not, and which hear not, and know not: and the God in whose hand are your breath, and all your ways has you not glorified.
A maimakon, sai ka nuna wa Ubangiji na sama girman kai. Ka sa aka kawo maka su kwaf na zinariya daga haikalinsa, da kai da hakimanka, da matanka da ƙwarƙwaranka kuka sha ruwan inabi da su. Kuka yabi allolin zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba sa ji, ba sa gani, ba sa da gane kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa.
24 Therefore from his presence has been sent forth the knuckle of a hand; and he has ordered the writing.
Saboda haka ya aiko da hannun da ya yi rubutun nan.
25 And this is the ordered writing, Mane, Thekel, Phares.
“Wannan shi ne rubutun da aka yi, Mene, mene, tekel, farsin
26 This is the interpretation of the sentence: Mane; God has measured your kingdom, and finished it.
“Abin da kalmomin nan suke nufi shi ne, “Mene, Allah ya ƙayyade yawan kwanakin mulkinka ya kuma kawo su ga ƙarshe.
27 Thekel; it has been weighed in the balance, and found lacking.
“Tekel, An kuma auna ka a ma’auni aka tarar ka kāsa.
28 Phares; your kingdom is divided, and given to the Medes and Persians.
“Feres, An raba mulkinka aka ba wa Medes da Farisa.”
29 Then Baltasar commanded, and they clothed Daniel with scarlet, and put the golden chain about his neck, and proclaimed concerning him that he was the third ruler in the kingdom.
Sai Belshazar ya umarta, aka sa wa Daniyel riga mai shunayya, aka sa sarƙar zinariya a wuyansa, aka kuma yi shela, cewa yanzu shi ne na uku a cikin masu mulkin ƙasar.
30 In the same night was Baltasar the Chaldean king slain.
A wannan dare aka kashe Belshazar, sarkin Babiloniyawa,
31 And Darius the Mede succeeded to the kingdom, being sixty-two years [old].
Dariyus mutumin Medes kuwa ya karɓi mulkin, yana da shekara sittin da biyu.

< Daniel 5 >