< Amos 7 >

1 Thus has the Lord God showed me; and, behold, a swarm of locusts coming from the east; and, behold, one caterpillar, king Gog.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
2 And it came to pass when he had finished devouring the grass of the land, that I said, Lord God, be merciful; who shall raise up Jacob? for he is small in number.
Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
3 Repent, O Lord, for this. And this shall not be, says the Lord.
Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
4 Thus has the Lord showed me; and, behold, the Lord called for judgment by fire, and it devoured the great deep, and devoured the Lord's portion.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
5 Then I said, O Lord, cease, I pray you: who shall raise up Jacob? for he is small in number. Repent, O Lord, for this.
Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
6 This also shall not be, says the Lord.
Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
7 Thus the Lord showed me; and behold, he stood upon a wall of adamant, and in his hand [was] an adamant.
Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
8 And the Lord said to me, What see you, Amos? And I said, An adamant. And the Lord said to me, Behold, I appoint an adamant in the midst of my people Israel: I will not pass by them any more.
Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
9 And the joyful altars shall be abolished, and the sacrifices of Israel shall be set aside; and I will rise up against the house of Jeroboam with the sword.
“Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
10 Then Amasias the priest of Bethel sent to Jeroboam king of Israel, saying, Amos is forming conspiracies against you in the midst of the house of Israel: the land will be utterly unable to bear all his words.
Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
11 For thus says Amos, Jeroboam shall die by the sword, and Israel shall be led away captive from his land.
Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
12 And Amasias said to Amos, Go, seer, remove you into the land of Juda, and live there, and you shall prophesy there:
Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
13 but you shall no longer prophesy at Bethel: for it is the king's sanctuary, and it is the royal house.
Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
14 And Amos answered, and said to Amasias, I was not a prophet, nor the son of a prophet; but I was a herdman, and a gatherer of sycamore fruits.
Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
15 And the Lord took me from the sheep, and the Lord said to me, Go, and prophesy to my people Israel.
Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
16 And now hear the word of the Lord: You say, Prophesy not to Israel, and raise not a tumult against the house of Jacob.
Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
17 Therefore thus says the Lord; Your wife shall be a harlot in the city, and your sons and your daughters shall fall by the sword, and your land shall be measured with the line; and you shall die in an unclean land; and Israel shall be led captive out of his land. Thus has the Lord God showed me.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”

< Amos 7 >