< Chronicles II 2 >

1 And Solomon said that he would build a house to the name of the Lord, and a house for his kingdom.
Solomon ya ba da umarni don a gina haikali domin sunan Ubangiji da kuma fada wa kansa.
2 And Solomon gathered seventy thousand men that bore burdens, and eighty thousand hewers of stone in the mountain, and [there were] three thousand six hundred superintendents over them.
Ya ɗebi mutane dubu saba’in su zama’yan ɗauko, mutane dubu tamanin su zama masu fasa dutse a tuddai, da kuma mutane dubu uku da ɗari shida su zama masu lura da su.
3 And Solomon sent to Chiram king of Tyre, saying, Whereas you did deal [favourably] with David my father, and did send him cedars to build for himself a house to dwell in,
Solomon ya aika wannan saƙo ga Hiram sarkin Taya. “Ka aika mini gumaguman al’ul kamar yadda ka yi wa mahaifina Dawuda sa’ad da ka aika masa al’ul don yă gina fada yă zauna a ciki.
4 behold, I also his son am building a house to the name of the Lord my God, to consecrate it to him, to burn incense before him, and [to offer] show bread continually, and to offer up whole burnt offerings continually morning and evening, and on the sabbaths, and at the new moons, and at the feasts of the Lord our God: this [is] a perpetual [statute] for Israel.
Yanzu ina shirin ginin haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, in kuma keɓe shi gare shi don ƙona turare mai ƙanshi a gabansa, don kuma ajiyar burodi mai tsarki kullum, da kuma don miƙa hadayun ƙonawa kowace safiya, kowace yamma, da a Asabbatai da Sababbin Wata, da kuma a ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji Allahnmu. Wannan dawwammamiyar farilla ce don Isra’ila.
5 And the house which I am building [is to be] great: for the Lord our God [is] great beyond all gods.
“Haikalin da zan gina zai zama mai girma, domin Allahnmu ya fi dukan sauran alloli girma.
6 And who will be able to build him a house? for the heaven and heaven of heavens do not bear his glory: and who am I, that I should build him a house, save only to burn incense before him?
Amma wa zai iya gina haikali dominsa, shi wanda sammai, har ma da sama sammai, ba za su iya riƙe shi ba? To, wane ne ni da zan gina haikali dominsa, in ba dai wurin ƙona hadayu a gabansa ba?
7 And now send me a man wise and skilled to work in gold, and in silver, and in brass, and in iron, and in purple, and in scarlet, and in blue, and one that knows how to grave together with the craftsmen who are with me in Juda and in Jerusalem, which materials my father David prepared.
“Saboda haka sai ka aiko mini da mutum wanda ya gwanince a aiki da azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, da kuma shunayya, da garura, da shuɗɗan zare, da wanda kuma ya gwanince da aikin sassaƙa, domin yă yi aiki tare da gwanayen mutane da nake da su a Yahuda da Urushalima, waɗanda mahaifina Dawuda ya tanada.
8 And send me from Libanus cedar wood, and wood of juniper, and pine; for I know that your servants are skilled in cutting timber in Libanus: and, behold, your servants shall go with my servants,
“Ka kuma aika mini al’ul, fir da gumaguman algum daga Lebanon, gama na san cewa mutanenka sun gwanince a yakan katakai a can. Mutanena kuwa za su yi aiki tare da naka
9 to prepare timber for me in abundance: for the house which I am building [must be] great and glorious.
don su tanada mini katakai da yawa, domin haikalin da zan gina dole yă zama mai girma da kuma ƙasaitacce.
10 And, behold, I have given freely to your servants that work and cut the wood, corn for food, [even] twenty thousand measures of wheat, and twenty thousand measures of barley, and twenty thousand measures of wine, and twenty thousand measures of oil.
Zan ba wa bayinka masu yankan katakai waɗanda suka yanka katako, garwa niƙaƙƙen alkama dubu ashirin, garwan sha’ir dubu ashirin da randunan ruwan inabi dubu ashirin da kuma randunan man zaitun dubu ashirin.”
11 And Chiram king of Tyre answered in writing, and sent to Solomon, saying, Because the Lord loved his people, he made you king over them.
Hiram sarkin Taya ya amsa ta wurin rubuta wasiƙa zuwa ga Solomon. “Domin Ubangiji yana ƙaunar mutanensa, ya naɗa ka sarkinsu.”
12 And Chiram said, Blessed [be] the Lord God of Israel, who made heaven and earth, who has given to king David a wise son, and one endowed with knowledge and understanding, who shall build a house for the Lord, and a house for his kingdom.
Hiram ya ƙara da cewa, “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya yi sama da ƙasa! Ya ba Sarki Dawuda ɗa mai hikima, cike da wayo da kuma sani, wanda zai gina haikali domin Ubangiji da kuma fada wa kansa.
13 And now I have sent you a wise and understanding man [who belonged] to Chiram my father
“Zan aika maka Huram-Abi, wani gwani wanda ya iya aiki, kuma mai hikima,
14 (his mother [was] of the daughters of Dan, and his father [was] a Tyrian), skilled to work in gold, and in silver, and in brass, and in iron, and in stones and wood; and to weave with purple, and blue, and fine linen, and scarlet; and to engrave, and to understand every device, whatever you shall give him [to do] with your craftsmen, and the craftsmen of my lord David your father.
wanda mahaifiyarsa ta fito daga Dan, mahaifinsa kuma daga Taya. An horar da shi a aikin zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, dutse, itace, da kuma shuɗi, shunayya, garura, da lilin mai kyau. Ya gogu a kowane irin zāne-zāne, zai kuma iya yin kowane zānen da aka ba shi. Zai yi aiki tare da masu sana’arka, da kuma tare da waɗanda ranka yă daɗe, Dawuda mahaifinka ya tanada.
15 And now, the wheat, and the barley, and the oil, and the wine which my lord mentioned, let him send to his servants.
“Yanzu fa, bari ranka yă daɗe, yă aiko wa bayinsa alkama da sha’ir da kuma man zaitun da ruwan inabin da ka alkawarta,
16 And we will cut timber out of Libanus according to all your need, and we will bring it on rafts to the sea of Joppa, and you shall bring it to Jerusalem.
za mu kuwa yanka dukan gumagumai daga Lebanon da kake bukata za mu kuwa yi fitonsu ta teku, su gangara zuwa Yaffa. Za ka iya kwashe su daga can ka haura zuwa Urushalima.”
17 And Solomon gathered all the foreigners that were in the land of Israel, after the numbering with which David his father numbered them; and there were found a hundred and fifty-three thousand six hundred.
Solomon ya ƙidaya dukan baƙin da suke cikin Isra’ila, bayan ƙidayan da mahaifinsa Dawuda ya yi; aka kuma tarar sun kai 153,600.
18 And he made of them seventy thousand burden-bearers, and eighty thousand hewers of stone, and three thousand six hundred taskmasters over the people.
Ya sa 70,000 a cikinsu su zama’yan ɗauko, 80,000 kuma su zama masu fasan dutse a tuddai, sa’an nan 3,600 su zama shugabanni masu lura da aiki.

< Chronicles II 2 >