< Kings III 3 >

1 And the wisdom of Solomon abounded exceedingly beyond the wisdom of all the ancients, and beyond all the wise men of Egypt: and he took the daughter of Pharao, and brought her into the city of David, until he had finished building his own house, and the house of the Lord first, and the wall of Jerusalem round about.
Solomon ya haɗa kai da Fir’auna sarkin Masar, ya kuwa auri’yarsa. Ya kawo ta cikin Birnin Dawuda kafin yă gama ginin fadarsa, da haikalin Ubangiji, da kuma katanga kewaye da Urushalima.
2 Nevertheless the people burnt incense on the high places, because a house had not yet been built to the Lord.
A lokacin dai mutane suna miƙa hadaya a wurare a bisa tuddai, domin ba a riga an gina haikali saboda Sunan Ubangiji ba.
3 And Solomon loved the Lord, [so as] to walk in the ordinances of David his father; only he sacrificed and burnt incense on the high places.
Solomon ya ƙaunaci Ubangiji ta wurin yin tafiya bisa ga farillan mahaifinsa Dawuda, sai dai ya miƙa hadayu, ya kuma ƙone turare a wuraren nan na bisa tuddai.
4 And he arose and went to Gabaon to sacrifice there, for that [was] the highest place, and great: Solomon offered a whole burnt offering of a thousand [victims] on the altar in Gabaon.
Sai sarki Solomon ya tafi Gibeyon don yă miƙa hadayu, gama a can ne wuri mafi muhimmanci na sujada. Solomon kuwa ya miƙa hadayun ƙonawa guda dubu a kan wannan bagade.
5 And the Lord appeared to Solomon in a dream by night, and the Lord said to Solomon, Ask some petition for yourself.
A Gibeyon, Ubangiji ya bayyana ga Solomon da dare a mafarki, Allah ya ce, “Ka roƙi abin da kake so in ba ka.”
6 And Solomon said, You have dealt very mercifully with your servant David my father according as he walked before you in truth, and in righteousness, and in uprightness of heart with you, and you have kept for him this great mercy, to set his son upon his throne, as [it is] this day.
Solomon ya amsa ya ce, “Ka nuna alheri mai girma ga bawanka, mahaifina Dawuda domin ya yi aminci gare ka da adalci, ya kuma kasance da zuciya mai gaskiya. Ka ci gaba da wannan alheri mai girma gare shi, ka ba shi ɗa don yă zauna a kujerar sarautarsa a wannan rana.
7 And now, O Lord my God, you have appointed your servant in the room of David my father; and I am a little child, and know not my going out an my coming in.
“Yanzu, ya Ubangiji Allahna, ka sa bawanka a wurin mahaifina Dawuda. Amma ni ɗan yaro ne kawai, ban kuma san yadda zan yi ayyukana ba.
8 But your servant [is] in the midst of your people, whom you have chosen, a great people, which as this day can’t be numbered.
Bawanka yana nan a cikin mutanen da ka zaɓa, mutane masu girma, waɗanda suka wuce ƙirge, ko a lissafta.
9 You shall give therefore to your servant a heart to hear and to judge your people justly, and to discern between good and evil: for who will be able to judge this your great people?
Saboda haka ka ba bawanka zuciyar ganewa, don yă shugabanci mutanenka, yă kuma iya rarrabe tsakanin abin da yake daidai da abin da ba daidai ba. Gama wa zai iya shugabance wannan mutanenka masu girma haka?”
10 And it was pleasing before the Lord, that Solomon asked this thing.
Sai Ubangiji ya ji daɗi cewa Solomon ya roƙa wannan.
11 And the Lord said to him, Because you have asked this thing of me, and have not asked for yourself long life, and have not asked wealth, nor have asked the lives of your enemies, but have asked for yourself understanding to hear judgment;
Saboda haka Allah ya ce masa, “Da yake ka nemi wannan ne, ba ka kuwa nemi tsawon rai ko arziki wa kanka ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, amma ka nemi ganewa a aikata gaskiya,
12 behold, I have done according to your word: behold, I have given you an understanding and wise heart: there has not been [any one] like you before you, and after you there shall not arise one like you.
zan yi abin da ka roƙa. Zan ba ka zuciya mai hikima da ta ganewa, har yă zama ba a taɓa samun wani kamar ka ba, ba kuwa za a taɓa samunsa ba.
13 And I have given you what you have not asked, wealth and glory, so that there has not been any one like you among kings.
Ban da haka ma, zan ba ka abin da ba ka nema ba; arziki da girma, don a rayuwarka ba za ka kasance da wani kamar ka ba a cikin sarakuna.
14 And if you will walk in my way, to keep my commandments and my ordinances, as David your father walked, then will I multiply your days.
In kuma ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi biyayya da farillaina da umarnaina kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, zan ba ka tsawon rai.”
15 And Solomon awoke, and, behold, [it was] a dream: and he arose and came to Jerusalem, and stood before the altar that was in front of the ark of the covenant of the Lord in Sion: and he offered whole burnt offerings, and sacrificed peace-offerings, and made a great banquet for himself and all his servants.
Sai Solomon ya farka, ya gane ashe mafarki ne. Ya koma Urushalima, ya tsaya a gaban akwatin alkawarin Ubangiji ya miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama. Sa’an nan ya shirya wa fadawansa biki.
16 Then there appeared two harlots before the king, and they stood before him.
To, ana nan sai waɗansu karuwai biyu suka zo wurin sarki, suka tsaya a gabansa.
17 And the one woman said, Hear me, [my] lord; I and this woman lived in one house, and we were delivered in the house.
Sai ɗaya ta ce, “Ranka yă daɗe, wannan mata da ni muna zama a gida ɗaya. Na haifi jariri yayinda take can tare da ni.
18 And it came to pass on the third day after I was delivered, this woman also was delivered: and we [were] together; and there was no one with us besides our two selves in the house.
Kwana uku bayan haihuwar jaririna, wannan mata ma ta haifi jariri. Mu dai kaɗai ne; babu wani a gidan sai mu biyu.
19 And this woman's child died in the night; because she overlaid it.
“Da dare ɗan wannan matan ya mutu domin ta kwanta a kansa.
20 and she arose in the middle of the night, and took my son from my arms, and laid him in her bosom, and laid her dead son in my bosom.
Saboda haka ta tashi da tsakar dare ta ɗauki ɗana daga gefena yayinda baiwarka take barci. Sai ta sa shi kusa da ƙirjinta, ta kuma sa mataccen ɗanta kusa da ƙirjina.
21 and I arose in the morning to suckle my son, and he was dead: and, behold, I considered him in the morning, and, behold, it was not my son whom I bore.
Kashegari, da na farka don in shayar da ɗana, sai na tarar ya mutu! Amma sa’ad da na dube shi da kyau da safe, sai na ga ashe ba ɗan da na haifa ba ne.”
22 And the other woman said, No, but the living [is] my son, and the dead [is] your son. So they spoke before the king.
Amma ɗaya matar ta ce, “A’a! Mai rai ɗin ne ɗana; mataccen naki ne.” Amma ta farin ta nace, “A’a! Mataccen ne naki; mai ran ne nawa.” A haka suka yi ta gardama a gaban sarki.
23 and the king said to them, You say, This [is] my son, [even] the living [one], and this woman's son [is] the dead one: and you say, No, but the living [is] my son, and the dead [is] your son.
Sarki ya ce, “Wannan ta ce, ‘Ɗana ne a raye, naki ne matacce,’ yayinda ɗayan tana cewa, ‘A’a! Ɗanki ne mataccen, nawa ne a raye.’”
24 And the king said, Fetch a sword. And they brought a sword before the king.
Sai sarki ya ce, “Kawo mini takobi.” Sai aka kawo takobi wa sarki.
25 And the king said, Divide the live child, the suckling, in two; and give half of it to one, and half of it to the other.
Ya ba da umarni ya ce, “Yanka yaron nan mai rai, gida biyu, kowacce ta ɗauki rabi.”
26 And the woman whose the living child was, answered and said to the king, (for her bowels yearned over her son) and she said, I pray you, [my] lord, give her the child, and in nowise kill it. But the other said, Let it be neither mine nor hers; divide [it].
Ainihin mamar ɗan da yake a raye ta cika da tausayi saboda ɗanta, sai ta ce wa sarki, “Ina roƙonka, ranka yă daɗe, kada ka kashe yaron! Ka ba ta kawai!” Amma ɗayan matar ta ce, “Kada a ba kowa daga cikinmu ɗan da rai, a ci gaba a raba shi!”
27 Then the king answered and said, Give the child to her that said, 'Give it to her, and by no means kill it:' she [is] its mother.
Sai sarki ya zartar da hukuncinsa ya ce, “A ba da jariri mai ran ga mata ta fari. Kada a kashe shi; ita ce ainihin mahaifiyarsa.”
28 and all Israel heard this judgment which the king judged, and they feared before the king; because they saw that the wisdom of God [was] in him, to execute judgment.
Sa’ad da dukan Isra’ila suka ji hukuncin da sarki ya zartar, suka girmama sarki sosai, domin sun gane cewa Allah ya ba shi hikimar yin shari’ar adalci.

< Kings III 3 >