< Chronicles I 12 >

1 And these [are] they that came to Sikelag, when he yet kept himself close because of Saul the son of Kis; and these [were] among the mighty, aiding [him] in war,
Waɗannan su ne mutanen da suka zo wurin Dawuda a Ziklag, yayinda aka kore shi daga gaban Shawulu ɗan Kish (suna cikin jarumawan da suka taimake shi a yaƙi;
2 and [using] the bow with the right hand and with the left, and slingers with stones, and [shooters] with bows. Of the brethren of Saul of Benjamin,
suna da baka suna kuma iya harba kibiya, ko majajjawa da hannun dama ko na hagu; su’yan’uwan Shawulu ne daga kabilar Benyamin):
3 the chief [was] Achiezer, and Joas son of Asma the Gabathite, and Joel and Jophalet, sons of Asmoth, and Berchia, and Jeul of Anathoth,
Ahiyezer babbansu da Yowash’ya’yan Shema’a maza daga Gibeya; Yeziyel da Felet’ya’yan Azmawet; Beraka, Yehu daga Anatot,
4 and Samaias the Gabaonite a mighty man among the thirty, and over the thirty; [and] Jeremia, and Jeziel, and Joanan, and Jozabath of Gadarathiim,
da Ishmahiya daga Gibeyon, wani jarumi a cikin Talatin nan, wanda shi ne shugaban Talatin; Irmiya, Yahaziyel, Yohanan, Yozabad daga Gedera,
5 Azai and Arimuth, and Baalia, and Samaraia, and Saphatias of Charaephiel,
Eluzai, Yerimot, Beyaliya, Shemariya da Shefatiya daga Haruf;
6 Helcana, and Jesuni, and Ozriel, and Jozara, and Sobocam, and the Corites,
Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezer da Yashobeyam daga Kora;
7 and Jelia and Zabadia, sons of Iroam, and the [men] of Gedor.
da Yoyela da Zebadiya’ya’yan Yeroham maza daga Gedor.
8 And from Gad these separated themselves to David from the wilderness, strong mighty men of war, bearing shields and spears, and their faces [were as] the face of a lion, and they were nimble as roes upon the mountains in speed.
Sai waɗansu mutanen Gad suka koma suna goyon bayan Dawuda suka kuma haɗa kai da shi a kagararsa a hamada. Su ƙwararrun mayaƙa ne, a shirye don yaƙi, kuma suna iya riƙe garkuwa da māshi. Fuskokinsu kamar fuskoki zakoki, kuma suna da sauri kamar bareyi a kan duwatsu.
9 Aza the chief, Abdia the second, Eliab the third,
Ezer shi ne babba, Obadiya shi ne mai binsa a shugabanci, Eliyab na uku,
10 Masmana the fourth, Jeremias the fifth,
Mismanna na huɗu, Irmiya na biyar,
11 Jethi the sixth, Eliab the seventh,
Attai na shida, Eliyel na bakwai,
12 Joanan the eighth, Eleazer the ninth,
Yohanan na takwas, Elzabad na tara,
13 Jeremia the tenth, Melchabanai the eleventh.
Irmiya na goma da kuma Makbannai na goma sha ɗaya.
14 These [were] chiefs of the army of the sons of Gad, the least one commander of a hundred, and the greatest one of a thousand.
Waɗannan mutanen Gad shugabannin mayaƙa ne; ƙarami a cikinsu zai iya ƙara da mutum ɗari, kuma babba a cikin zai iya ƙara da dubu.
15 These [are] the [men] that crossed over Jordan in the first month, and it had overflowed all its banks; and they drove out all the inhabitants of the valleys, from the east to the west.
Su ne suka haye Urdun a wata na farko sa’ad da kogin ya yi ambaliya, suka kuma kori duk mai rai a kwarin, na wajen gabas da na wajen yamma.
16 And there came [some] of the sons of Benjamin and Juda to the assistance of David.
Sauran mutanen Benyamin da waɗansu mutanen Yahuda su ma suka zo wurin Dawuda a kagararsa.
17 And David went out to meet them, and said to them, If you are come peaceably to me, let my heart be at peace with you: but if [you are come] to betray me to my enemies unfaithfully, the God of your fathers look upon it, and reprove it.
Sai Dawuda ya fita don yă tarye su, ya kuma ce musu, “In kun zo wurina da salama, don ku taimake ni, to, ina a shirye in bar ku ku haɗa kai tare da ni. Amma in kun zo don ku bashe ni ga abokan gābana sa’ad da hannuwana ba su da laifi a rikici, bari Allah na kakanninmu yă duba yă kuma shari’anta ku.”
18 And the Spirit came upon Amasai, a captain of the thirty, and he said, Go, David, son of Jesse, you and your people, peace, peace be to you, and peace to your helpers, for your God has helped you. And David received them, and made them captains of the forces.
Sai Ruhu ya sauko a kan Amasai, shugaban Talatin nan, sai ya ce, “Mu naka ne, ya Dawuda! Muna tare da kai, ya ɗan Yesse! Nasara, nasara gare ka, nasara kuma ga waɗanda suke taimakonka. Gama Allahnka zai taimake ka.” Saboda haka Dawuda ya karɓe su ya kuma mai da su shugabannin ƙungiyoyin maharansa.
19 And [some] came to David from Manasse, when the Philistines came against Saul to war: and he helped them not, because the captains of the Philistines took counsel, saying, With the heads of those men will he return to his master Saul.
Waɗansu mutanen Manasse suka haɗa kai da Dawuda sa’ad da ya tafi tare da Filistiyawa don yă yaƙi Shawulu (Shi da mutanensa ba su taimaki Filistiyawa ba domin bayan shawarwari, shugabanninsu suka salame shi. Sun ce, “Za mu biya da kawunanmu in ya koma ga maigidansa Shawulu.”)
20 When David was going to Sikelag, there came to him of Manasse, Edna and Jozabath, and Rodiel, and Michael, and Josabaith, and Elimuth, and Semathi: [these] are the captains of thousands of Manasse.
Da Dawuda ya tafi Ziklag, waɗannan mutanen Manasse ne suka haɗa kai da shi. Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika’ilu, Yozabad, Elihu da Zilletai, shugabannin ƙungiyoyi na dubu a cikin Manasse.
21 And they fought on the side of David against a troop, for they [were] all men of might; and they were commanders in the army, [because] of [their] might.
Suka taimaki Dawuda a kan ƙungiyoyin hari, gama dukansu jarumawa ne sosai, kuma su shugabanni ne a cikin mayaƙansa.
22 For daily men came to David, [till they amounted] to a great force, as the force of God.
Kowace rana mutane suka riƙa zuwa don su taimaki Dawuda, sai da ya kasance da runduna mai girma, kamar mayaƙan Allah.
23 And these [are] the names of the commanders of the army, who came to David to Chebron, to turn the kingdom of Saul to him according to the word of the Lord.
Ga yawan mutanen shiryayyu don yaƙi waɗanda suka zo wurin Dawuda a Hebron don su mai da mulkin Shawulu gare shi, yadda Ubangiji ya faɗa.
24 The sons of Juda, bearing shields and spears, six thousand and eight hundred mighty in war.
Mutanen Yahuda, masu riƙe garkuwa da māshi, su 6,800 shiryayyu don yaƙi;
25 Of the sons of Symeon mighty for battle, seven thousand and a hundred.
mutanen Simeyon, jarumawa shiryayyu don yaƙi, su 7,100;
26 Of the sons of Levi, four thousand and six hundred.
mutanen Lawi, su 4,600,
27 And Joadas the chief [of the family] of Aaron, and with him three thousand and seven hundred.
haɗe da Yehohiyada, shugaban iyalin Haruna tare da mutane 3,700,
28 And Sadoc, a young [man] mighty in strength, and [there were] twenty-two leaders of his father's house.
da Zadok, matashi jarumi sosai, tare da shugabanni su 22 daga iyalinsa;
29 And of the sons of Benjamin, the brethren of Saul, three thousand: and still the greater part of them kept the guard of the house of Saul.
mutanen Benyamin,’yan’uwan Shawulu, su 3,000, yawanci waɗanda suke biyayya ga gidan Shawulu sai lokacin;
30 And of the sons of Ephraim, twenty thousand and eight hundred mighty men, famous in the houses of their fathers.
mutanen Efraim, jarumawa, sanannu cikin gidajensu, su 20 800;
31 And of the half-tribe of Manasse, eighteen thousand, even [those] who were named by name, to make David king.
mutanen rabin kabilar Manasse, sanannu da sunaye suka zo suka mai da Dawuda sarki, su 18,000;
32 And of the sons of Issachar having wisdom with regard to the times, knowing what Israel should do, two hundred; and all their brethren with them.
mutanen Issakar, masu fahimtar lokuta suka kuma san abin da ya kamata Isra’ila ya yi, manya 200, tare da danginsu a ƙarƙashin shugabancinsu;
33 And of Zabulon they that went out to battle, with all weapons of war, [were] fifty thousand to help David, not weak-handed.
mutanen Zebulun, ƙwararru sojoji shiryayyu don yaƙi da kowane irin makami, suka zo don su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya, su 50,000;
34 And of Nephthali a thousand captains, and with them [men] with shields and spears, thirty-seven thousand.
mutanen Naftali su 1,000 shugabanni, tare da mutane 37,000 masu riƙe garkuwa da masu;
35 And of the Danites [men] ready for war twenty-eight thousand and eight hundred.
mutanen Dan, shiryayyu don yaƙi, su 28,600;
36 And of Aser, they that went out to give aid in war, forty thousand.
mutanen Asher, ƙwararrun sojoji shiryayyu don yaƙi, su 40,000;
37 And from the country beyond Jordan, from Ruben, and the Gadites, and from the half-tribe of Manasse, a hundred and twenty thousand, with all weapons of war.
kuma daga gabashin Urdun, mutanen Ruben, Gad da kuma rabin kabilar Manasse, masu kayan yaƙi iri-iri, su 120,000.
38 All these [were] men of war, setting [the army] in battle array, with a peaceful mind [towards him], and they came to Chebron to make David king over all Israel: and the rest of Israel [were of] one mind to make David king.
Dukan waɗannan mayaƙa ne waɗanda suka ba da kansu da yardar rai su yi hidima. Suka zo Hebron da cikakken niyya don su naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila. Duka sauran Isra’ilawa su ma suka goyi baya a naɗa Dawuda sarki.
39 And they were there three days eating and drinking, for their brethren [had] made preparations.
Mutanen suka yi kwana uku a can tare da Dawuda, suna ci suna sha, gama iyalansu sun yi musu tanadi.
40 And their neighbors, as far as Issachar and Zabulon and Nephthali, brought to them upon camels, and asses, and mules, and upon calves, food, meal, cakes of figs, raisins, wine, and oil, calves and sheep abundantly: for [there was] joy in Israel.
Haka ma, maƙwabtansu daga nesa har Issakar, Zebulun da Naftali suka zo suka kawo abinci a kan jakuna, raƙuma, alfadarai da shanu. Akwai tanadin mai yawa na gari, kauɗar ɓaure, nonnan busassun’ya’yan inabi, ruwan inabi, mai, shanu da tumaki. Duk an yi haka don a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra’ila.

< Chronicles I 12 >