< Psalms 90 >

1 A Prayer of Moses the man of God. Lord, thou hast been our dwelling place in all generations.
Addu’ar Musa Mutumin Allah. Ubangiji kai ne mazauninmu cikin dukan zamanai.
2 Before the mountains were brought forth, or ever thou hadst formed the earth and the world, even from everlasting to everlasting, thou [art] God.
Kafin a haifi duwatsu ko a fid da ƙasa da duniya, daga madawwami zuwa madawwami kai Allah ne.
3 Thou turnest man to destruction; and sayest, Return, ye children of men.
Ka komar da mutane zuwa ƙura, kana cewa, “Ku koma ƙura, ya ku’ya’yan mutane.”
4 For a thousand years in thy sight [are but] as yesterday when it is past, and [as] a watch in the night.
Gama shekaru dubu a gabanka kamar kwana ɗaya ne da ya wuce, ko sa’a guda na dare.
5 Thou carriest them away as with a flood; they are [as] a sleep: in the morning [they are] like grass [which] groweth up.
Ka share mutane cikin barcin mutuwa; suna kama da sabuwa ciyawar safiya,
6 In the morning it flourisheth, and groweth up; in the evening it is cut down, and withereth.
ko da yake da safe takan yi sabuwar huda da yamma sai ta bushe ta kuma yanƙwane.
7 For we are consumed by thine anger, and by thy wrath are we troubled.
An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.
8 Thou hast set our iniquities before thee, our secret [sins] in the light of thy countenance.
Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
9 For all our days are passed away in thy wrath: we spend our years as a tale [that is told].
Dukan kwanakinmu sun wuce ƙarƙashin fushinka; mun gama shekarunmu da nishi.
10 The days of our years [are] threescore years and ten; and if by reason of strength [they be] fourscore years, yet [is] their strength labour and sorrow; for it is soon cut off, and we fly away.
Tsawon kwanakinmu shekaru saba’in ne, ko tamanin, in muna da ƙarfi; duk da haka tsawonsu wahaloli ne kawai da ɓacin rai, gama da sauri suke wucewa, ta mu kuma ta ƙare.
11 Who knoweth the power of thine anger? even according to thy fear, [so is] thy wrath.
Wa ya san ƙarfin fushinka? Gama hasalarka tana da girma kamar tsoron da ya dace da kai.
12 So teach [us] to number our days, that we may apply [our] hearts unto wisdom.
Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
13 Return, O LORD, how long? and let it repent thee concerning thy servants.
Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
14 O satisfy us early with thy mercy; that we may rejoice and be glad all our days.
Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
15 Make us glad according to the days [wherein] thou hast afflicted us, [and] the years [wherein] we have seen evil.
Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
16 Let thy work appear unto thy servants, and thy glory unto their children.
Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga’ya’yansu.
17 And let the beauty of the LORD our God be upon us: and establish thou the work of our hands upon us; yea, the work of our hands establish thou it.
Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.

< Psalms 90 >