< Psalms 87 >

1 A Psalm [or] Song for the sons of Korah. His foundation [is] in the holy mountains.
Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.
2 The LORD loveth the gates of Zion more than all the dwellings of Jacob.
Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.
3 Glorious things are spoken of thee, O city of God. (Selah)
Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, (Sela)
4 I will make mention of Rahab and Babylon to them that know me: behold Philistia, and Tyre, with Ethiopia; this [man] was born there.
“Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’”
5 And of Zion it shall be said, This and that man was born in her: and the highest himself shall establish her.
Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”
6 The LORD shall count, when he writeth up the people, [that] this [man] was born there. (Selah)
Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” (Sela)
7 As well the singers as the players on instruments [shall be there: ] all my springs [are] in thee.
Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”

< Psalms 87 >