< Psalms 77 >

1 To the chief Musician, to Jeduthun, A Psalm of Asaph. I cried unto God with my voice, [even] unto God with my voice; and he gave ear unto me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
2 In the day of my trouble I sought the Lord: my sore ran in the night, and ceased not: my soul refused to be comforted.
Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
3 I remembered God, and was troubled: I complained, and my spirit was overwhelmed. (Selah)
Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
4 Thou holdest mine eyes waking: I am so troubled that I cannot speak.
ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
5 I have considered the days of old, the years of ancient times.
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6 I call to remembrance my song in the night: I commune with mine own heart: and my spirit made diligent search.
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
7 Will the Lord cast off for ever? and will he be favourable no more?
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8 Is his mercy clean gone for ever? doth [his] promise fail for evermore?
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9 Hath God forgotten to be gracious? hath he in anger shut up his tender mercies? (Selah)
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
10 And I said, This [is] my infirmity: [but I will remember] the years of the right hand of the most High.
Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
11 I will remember the works of the LORD: surely I will remember thy wonders of old.
Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
12 I will meditate also of all thy work, and talk of thy doings.
Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
13 Thy way, O God, [is] in the sanctuary: who [is so] great a God as [our] God?
Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
14 Thou [art] the God that doest wonders: thou hast declared thy strength among the people.
Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
15 Thou hast with [thine] arm redeemed thy people, the sons of Jacob and Joseph. (Selah)
Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
16 The waters saw thee, O God, the waters saw thee; they were afraid: the depths also were troubled.
Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
17 The clouds poured out water: the skies sent out a sound: thine arrows also went abroad.
Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
18 The voice of thy thunder [was] in the heaven: the lightnings lightened the world: the earth trembled and shook.
Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
19 Thy way [is] in the sea, and thy path in the great waters, and thy footsteps are not known.
Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
20 Thou leddest thy people like a flock by the hand of Moses and Aaron.
Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.

< Psalms 77 >