< Psalms 61 >

1 To the chief Musician upon Neginah, [A Psalm] of David. Hear my cry, O God; attend unto my prayer.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
2 From the end of the earth will I cry unto thee, when my heart is overwhelmed: lead me to the rock [that] is higher than I.
Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
3 For thou hast been a shelter for me, [and] a strong tower from the enemy.
Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
4 I will abide in thy tabernacle for ever: I will trust in the covert of thy wings. (Selah)
Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
5 For thou, O God, hast heard my vows: thou hast given [me] the heritage of those that fear thy name.
Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
6 Thou wilt prolong the king’s life: [and] his years as many generations.
Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
7 He shall abide before God for ever: O prepare mercy and truth, [which] may preserve him.
Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
8 So will I sing praise unto thy name for ever, that I may daily perform my vows.
Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.

< Psalms 61 >