< Psalms 138 >

1 [A Psalm] of David. I will praise thee with my whole heart: before the gods will I sing praise unto thee.
Ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; a gaban “alloli” zan rera yabo.
2 I will worship toward thy holy temple, and praise thy name for thy lovingkindness and for thy truth: for thou hast magnified thy word above all thy name.
Zan rusuna ta wajen haikalinka mai tsarki zan kuma yabi sunanka saboda ƙaunarka da amincinka, saboda ka ɗaukaka a bisa kome sunanka da kuma maganarka.
3 In the day when I cried thou answeredst me, [and] strengthenedst me [with] strength in my soul.
Sa’ad da na kira, ka amsa mini; ka sa na zama mai ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa ni.
4 All the kings of the earth shall praise thee, O LORD, when they hear the words of thy mouth.
Bari dukan sarakunan duniya su yabe ka, ya Ubangiji, sa’ad da suka ji maganganun bakinka.
5 Yea, they shall sing in the ways of the LORD: for great [is] the glory of the LORD.
Bari su rera game da hanyoyin Ubangiji, gama ɗaukakar Ubangiji da girma take.
6 Though the LORD [be] high, yet hath he respect unto the lowly: but the proud he knoweth afar off.
Ko da yake Ubangiji yana bisa, yakan dubi kāsassu, amma tun da nesa ya san masu girman kai.
7 Though I walk in the midst of trouble, thou wilt revive me: thou shalt stretch forth thine hand against the wrath of mine enemies, and thy right hand shall save me.
Ko da na yi tafiya a tsakiyar wahala, kana kiyaye raina; ka miƙa hannunka a kan fushin maƙiyana, da hannunka na dama ka cece ni.
8 The LORD will perfect [that which] concerneth me: thy mercy, O LORD, [endureth] for ever: forsake not the works of thine own hands.
Ubangiji zai cika manufarsa a kaina; ƙaunarka, ya Ubangiji, madawwamiya ce har abada, kada ka ƙyale ayyukan hannuwanka.

< Psalms 138 >