< Psalms 122 >
1 A Song of degrees of David. I was glad when they said unto me, Let us go into the house of the LORD.
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
2 Our feet shall stand within thy gates, O Jerusalem.
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
3 Jerusalem is builded as a city that is compact together:
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
4 Whither the tribes go up, the tribes of the LORD, unto the testimony of Israel, to give thanks unto the name of the LORD.
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
5 For there are set thrones of judgment, the thrones of the house of David.
A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
6 Pray for the peace of Jerusalem: they shall prosper that love thee.
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
7 Peace be within thy walls, [and] prosperity within thy palaces.
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
8 For my brethren and companions’ sakes, I will now say, Peace [be] within thee.
Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
9 Because of the house of the LORD our God I will seek thy good.
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.