< Psalms 105 >

1 O give thanks unto the LORD; call upon his name: make known his deeds among the people.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Sing unto him, sing psalms unto him: talk ye of all his wondrous works.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 Glory ye in his holy name: let the heart of them rejoice that seek the LORD.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 Seek the LORD, and his strength: seek his face evermore.
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Remember his marvellous works that he hath done; his wonders, and the judgments of his mouth;
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 O ye seed of Abraham his servant, ye children of Jacob his chosen.
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 He [is] the LORD our God: his judgments [are] in all the earth.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 He hath remembered his covenant for ever, the word [which] he commanded to a thousand generations.
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 Which [covenant] he made with Abraham, and his oath unto Isaac;
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 And confirmed the same unto Jacob for a law, [and] to Israel [for] an everlasting covenant:
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 Saying, Unto thee will I give the land of Canaan, the lot of your inheritance:
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 When they were [but] a few men in number; yea, very few, and strangers in it.
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 When they went from one nation to another, from [one] kingdom to another people;
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 He suffered no man to do them wrong: yea, he reproved kings for their sakes;
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 [Saying], Touch not mine anointed, and do my prophets no harm.
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 Moreover he called for a famine upon the land: he brake the whole staff of bread.
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 He sent a man before them, [even] Joseph, [who] was sold for a servant:
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 Whose feet they hurt with fetters: he was laid in iron:
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 Until the time that his word came: the word of the LORD tried him.
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 The king sent and loosed him; [even] the ruler of the people, and let him go free.
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 He made him lord of his house, and ruler of all his substance:
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 To bind his princes at his pleasure; and teach his senators wisdom.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 Israel also came into Egypt; and Jacob sojourned in the land of Ham.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 And he increased his people greatly; and made them stronger than their enemies.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 He turned their heart to hate his people, to deal subtilly with his servants.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 He sent Moses his servant; [and] Aaron whom he had chosen.
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 They shewed his signs among them, and wonders in the land of Ham.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 He sent darkness, and made it dark; and they rebelled not against his word.
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 He turned their waters into blood, and slew their fish.
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 Their land brought forth frogs in abundance, in the chambers of their kings.
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 He spake, and there came divers sorts of flies, [and] lice in all their coasts.
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 He gave them hail for rain, [and] flaming fire in their land.
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 He smote their vines also and their fig trees; and brake the trees of their coasts.
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 He spake, and the locusts came, and caterpillers, and that without number,
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 And did eat up all the herbs in their land, and devoured the fruit of their ground.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 He smote also all the firstborn in their land, the chief of all their strength.
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 He brought them forth also with silver and gold: and [there was] not one feeble [person] among their tribes.
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 Egypt was glad when they departed: for the fear of them fell upon them.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 He spread a cloud for a covering; and fire to give light in the night.
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 [The people] asked, and he brought quails, and satisfied them with the bread of heaven.
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 He opened the rock, and the waters gushed out; they ran in the dry places [like] a river.
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 For he remembered his holy promise, [and] Abraham his servant.
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 And he brought forth his people with joy, [and] his chosen with gladness:
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 And gave them the lands of the heathen: and they inherited the labour of the people;
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 That they might observe his statutes, and keep his laws. Praise ye the LORD.
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< Psalms 105 >