< Psalms 102 >

1 A Prayer of the afflicted, when he is overwhelmed, and poureth out his complaint before the LORD. Hear my prayer, O LORD, and let my cry come unto thee.
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 Hide not thy face from me in the day [when] I am in trouble; incline thine ear unto me: in the day [when] I call answer me speedily.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 For my days are consumed like smoke, and my bones are burned as an hearth.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 My heart is smitten, and withered like grass; so that I forget to eat my bread.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 By reason of the voice of my groaning my bones cleave to my skin.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 I am like a pelican of the wilderness: I am like an owl of the desert.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 I watch, and am as a sparrow alone upon the house top.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 Mine enemies reproach me all the day; [and] they that are mad against me are sworn against me.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 For I have eaten ashes like bread, and mingled my drink with weeping,
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 Because of thine indignation and thy wrath: for thou hast lifted me up, and cast me down.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 My days [are] like a shadow that declineth; and I am withered like grass.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 But thou, O LORD, shalt endure for ever; and thy remembrance unto all generations.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Thou shalt arise, [and] have mercy upon Zion: for the time to favour her, yea, the set time, is come.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 For thy servants take pleasure in her stones, and favour the dust thereof.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 So the heathen shall fear the name of the LORD, and all the kings of the earth thy glory.
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 When the LORD shall build up Zion, he shall appear in his glory.
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 He will regard the prayer of the destitute, and not despise their prayer.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 This shall be written for the generation to come: and the people which shall be created shall praise the LORD.
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 For he hath looked down from the height of his sanctuary; from heaven did the LORD behold the earth;
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 To hear the groaning of the prisoner; to loose those that are appointed to death;
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 To declare the name of the LORD in Zion, and his praise in Jerusalem;
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 When the people are gathered together, and the kingdoms, to serve the LORD.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 He weakened my strength in the way; he shortened my days.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 I said, O my God, take me not away in the midst of my days: thy years [are] throughout all generations.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 Of old hast thou laid the foundation of the earth: and the heavens [are] the work of thy hands.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 They shall perish, but thou shalt endure: yea, all of them shall wax old like a garment; as a vesture shalt thou change them, and they shall be changed:
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 But thou [art] the same, and thy years shall have no end.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 The children of thy servants shall continue, and their seed shall be established before thee.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”

< Psalms 102 >