< Proverbs 6 >

1 My son, if thou be surety for thy friend, [if] thou hast stricken thy hand with a stranger,
Ɗana, in ka shirya tsaya wa maƙwabcinka don yă karɓi bashi, in ka sa hannunka don ɗaukar lamunin wani,
2 Thou art snared with the words of thy mouth, thou art taken with the words of thy mouth.
in maganarka ta taɓa kama ka, ko kalmomin bakinka sun zama maka tarko,
3 Do this now, my son, and deliver thyself, when thou art come into the hand of thy friend; go, humble thyself, and make sure thy friend.
to, sai ka yi haka, ɗana don ka’yantar da kanka; da yake ka shiga hannuwan maƙwabcinka, ka tafi ka ƙasƙantar da kanka; ka roƙi maƙwabcinka!
4 Give not sleep to thine eyes, nor slumber to thine eyelids.
Ka hana kanka barci, ko gyangyaɗi a idanunka ma.
5 Deliver thyself as a roe from the hand [of the hunter], and as a bird from the hand of the fowler.
Ka’yantar da kanka, kamar barewa daga hannun mai farauta, kamar tsuntsu daga tarkon mai kafa tarko.
6 Go to the ant, thou sluggard; consider her ways, and be wise:
Ku tafi wurin kyashi, ku ragwaye; ku lura da hanyoyinsa ku zama masu hikima!
7 Which having no guide, overseer, or ruler,
Ba shi da jagora ba shugaba ko mai mulki,
8 Provideth her meat in the summer, [and] gathereth her food in the harvest.
duk da haka yakan yi tanade-tanadensa da rani ya kuma tattara abincinsa a lokacin girbi.
9 How long wilt thou sleep, O sluggard? when wilt thou arise out of thy sleep?
Har yaushe za ku kwanta a can, ku ragwaye? Yaushe za ku farka daga barcinku?
10 [Yet] a little sleep, a little slumber, a little folding of the hands to sleep:
Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
11 So shall thy poverty come as one that travelleth, and thy want as an armed man.
talauci kuwa zai zo kamar’yan hari rashi kuma kamar ɗan fashi.
12 A naughty person, a wicked man, walketh with a froward mouth.
Sakare da mutumin banza wanda yana yawo da magana banza a baki,
13 He winketh with his eyes, he speaketh with his feet, he teacheth with his fingers;
wanda yake ƙyifce da ido, yana yi alama da ƙafafunsa yana kuma nuni da yatsotsinsa,
14 Frowardness [is] in his heart, he deviseth mischief continually; he soweth discord.
wanda yake ƙulla mugunta da ruɗu a cikin zuciyarsa, kullum yana tā-da-na-zaune-tsaye
15 Therefore shall his calamity come suddenly; suddenly shall he be broken without remedy.
Saboda haka masifa za tă fāɗa farat ɗaya; za a hallaka shi nan da nan, ba makawa.
16 These six [things] doth the LORD hate: yea, seven [are] an abomination unto him:
Akwai abubuwa shida da Ubangiji ya ƙi, abubuwa bakwai da suke abin ƙyama gare shi,
17 A proud look, a lying tongue, and hands that shed innocent blood,
duban reni, harshe mai ƙarya, hannuwa masu zub da jinin marar laifi,
18 An heart that deviseth wicked imaginations, feet that be swift in running to mischief,
zuciyar da take ƙulla mugayen dabaru, ƙafafun da suke sauri zuwa aikata mugunta,
19 A false witness [that] speaketh lies, and he that soweth discord among brethren.
mai shaidar ƙarya wanda yake zuba ƙarairayi, da kuma mutumin da yake tā-da-na-zaune-tsaye a cikin’yan’uwa.
20 My son, keep thy father’s commandment, and forsake not the law of thy mother:
Ɗana, ka kiyaye umarnan mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
21 Bind them continually upon thine heart, [and] tie them about thy neck.
Ka ɗaura su a zuciyarka har abada; ka ɗaura su kewaye da wuyanka.
22 When thou goest, it shall lead thee; when thou sleepest, it shall keep thee; and [when] thou awakest, it shall talk with thee.
Sa’ad da kake tafiya, za su bishe ka; sa’ad da kake barci, za su lura da kai; sa’ad da ka farka, za su yi maka magana.
23 For the commandment [is] a lamp; and the law [is] light; and reproofs of instruction [are] the way of life:
Gama waɗannan umarnai fitila ne, wannan koyarwa haske ne, kuma gyare-gyaren horo hanyar rayuwa ce,
24 To keep thee from the evil woman, from the flattery of the tongue of a strange woman.
suna kiyaye ka daga mace marar ɗa’a daga sulɓin harshen mace marar aminci.
25 Lust not after her beauty in thine heart; neither let her take thee with her eyelids.
Kada ka yi sha’awarta a cikin zuciyarka kada ka bar ta tă ɗauki hankalinka da idanunta.
26 For by means of a whorish woman [a man is brought] to a piece of bread: and the adulteress will hunt for the precious life.
Gama karuwa takan mai da kai kamar burodin kyauta, mazinaciya kuma takan farauci ranka.
27 Can a man take fire in his bosom, and his clothes not be burned?
Mutum zai iya ɗiba wuta ya zuba a cinyarsa ba tare da rigunansa sun ƙone ba?
28 Can one go upon hot coals, and his feet not be burned?
Mutum zai iya yin tafi a garwashi wuta mai zafi ba tare da ƙafafunsa sun ƙone ba?
29 So he that goeth in to his neighbour’s wife; whosoever toucheth her shall not be innocent.
Haka yake da wanda ya kwana da matar wani; babu wanda ya taɓa ta da zai tafi babu hukunci.
30 [Men] do not despise a thief, if he steal to satisfy his soul when he is hungry;
Mutane ba sa ƙyale ɓarawo in ya yi sata don yă ƙosar da yunwarsa sa’ad da yake jin yunwa.
31 But [if] he be found, he shall restore sevenfold; he shall give all the substance of his house.
Duk da haka in aka kama shi, dole yă biya sau bakwai ko da yake abin zai ci dukan arzikin gidansa.
32 [But] whoso committeth adultery with a woman lacketh understanding: he [that] doeth it destroyeth his own soul.
Amma mutumin da ya yi zina ba shi da hankali; duk wanda ya yi haka yana hallaka kansa ne.
33 A wound and dishonour shall he get; and his reproach shall not be wiped away.
Dūka da kunya ne za su zama rabonsa, kuma kunyarsa za tă dawwama.
34 For jealousy [is] the rage of a man: therefore he will not spare in the day of vengeance.
Gama kishi kan tā da hasalar miji, kuma ba zai ji tausayi ba sa’ad da yake ramawa.
35 He will not regard any ransom; neither will he rest content, though thou givest many gifts.
Ba zai karɓi duk wata biya ba; zai ƙi cin hanci, kome yawansu.

< Proverbs 6 >