< Mark 3 >

1 And he entered again into the synagogue; and there was a man there which had a withered hand.
Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
2 And they watched him, whether he would heal him on the sabbath day; that they might accuse him.
Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
3 And he saith unto the man which had the withered hand, Stand forth.
Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
4 And he saith unto them, Is it lawful to do good on the sabbath days, or to do evil? to save life, or to kill? But they held their peace.
Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
5 And when he had looked round about on them with anger, being grieved for the hardness of their hearts, he saith unto the man, Stretch forth thine hand. And he stretched [it] out: and his hand was restored whole as the other.
Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
6 And the Pharisees went forth, and straightway took counsel with the Herodians against him, how they might destroy him.
Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
7 But Jesus withdrew himself with his disciples to the sea: and a great multitude from Galilee followed him, and from Judæa,
Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
8 And from Jerusalem, and from Idumaea, and [from] beyond Jordan; and they about Tyre and Sidon, a great multitude, when they had heard what great things he did, came unto him.
Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
9 And he spake to his disciples, that a small ship should wait on him because of the multitude, lest they should throng him.
Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
10 For he had healed many; insomuch that they pressed upon him for to touch him, as many as had plagues.
Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
11 And unclean spirits, when they saw him, fell down before him, and cried, saying, Thou art the Son of God.
Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
12 And he straitly charged them that they should not make him known.
Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
13 And he goeth up into a mountain, and calleth [unto him] whom he would: and they came unto him.
Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
14 And he ordained twelve, that they should be with him, and that he might send them forth to preach,
Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
15 And to have power to heal sicknesses, and to cast out devils:
don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
16 And Simon he surnamed Peter;
Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
17 And James the [son] of Zebedee, and John the brother of James; and he surnamed them Boanerges, which is, The sons of thunder:
Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
18 And Andrew, and Philip, and Bartholomew, and Matthew, and Thomas, and James the [son] of Alphaeus, and Thaddaeus, and Simon the Canaanite,
Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
19 And Judas Iscariot, which also betrayed him: and they went into an house.
da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
20 And the multitude cometh together again, so that they could not so much as eat bread.
Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
21 And when his friends heard [of it], they went out to lay hold on him: for they said, He is beside himself.
Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
22 And the scribes which came down from Jerusalem said, He hath Beelzebub, and by the prince of the devils casteth he out devils.
Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
23 And he called them [unto him], and said unto them in parables, How can Satan cast out Satan?
Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
24 And if a kingdom be divided against itself, that kingdom cannot stand.
In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
25 And if a house be divided against itself, that house cannot stand.
In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
26 And if Satan rise up against himself, and be divided, he cannot stand, but hath an end.
In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
27 No man can enter into a strong man’s house, and spoil his goods, except he will first bind the strong man; and then he will spoil his house.
Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
28 Verily I say unto you, All sins shall be forgiven unto the sons of men, and blasphemies wherewith soever they shall blaspheme:
Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
29 But he that shall blaspheme against the Holy Ghost hath never forgiveness, but is in danger of eternal damnation: (aiōn g165, aiōnios g166)
Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn g165, aiōnios g166)
30 Because they said, He hath an unclean spirit.
Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
31 There came then his brethren and his mother, and, standing without, sent unto him, calling him.
Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
32 And the multitude sat about him, and they said unto him, Behold, thy mother and thy brethren without seek for thee.
Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
33 And he answered them, saying, Who is my mother, or my brethren?
Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
34 And he looked round about on them which sat about him, and said, Behold my mother and my brethren!
Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
35 For whosoever shall do the will of God, the same is my brother, and my sister, and mother.
Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”

< Mark 3 >