< Luke 21 >

1 And he looked up, and saw the rich men casting their gifts into the treasury.
Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
2 And he saw also a certain poor widow casting in thither two mites.
Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
3 And he said, Of a truth I say unto you, that this poor widow hath cast in more than they all:
Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
4 For all these have of their abundance cast in unto the offerings of God: but she of her penury hath cast in all the living that she had.
Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
5 And as some spake of the temple, how it was adorned with goodly stones and gifts, he said,
Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
6 [As for] these things which ye behold, the days will come, in the which there shall not be left one stone upon another, that shall not be thrown down.
“Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
7 And they asked him, saying, Master, but when shall these things be? and what sign [ will there be] when these things shall come to pass?
Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
8 And he said, Take heed that ye be not deceived: for many shall come in my name, saying, I am [Christ]; and the time draweth near: go ye not therefore after them.
Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
9 But when ye shall hear of wars and commotions, be not terrified: for these things must first come to pass; but the end [is] not by and by.
Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
10 Then said he unto them, Nation shall rise against nation, and kingdom against kingdom:
Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
11 And great earthquakes shall be in divers places, and famines, and pestilences; and fearful sights and great signs shall there be from heaven.
Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
12 But before all these, they shall lay their hands on you, and persecute [you], delivering [you] up to the synagogues, and into prisons, being brought before kings and rulers for my name’s sake.
“Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
13 And it shall turn to you for a testimony.
Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
14 Settle [it] therefore in your hearts, not to meditate before what ye shall answer:
Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
15 For I will give you a mouth and wisdom, which all your adversaries shall not be able to gainsay nor resist.
Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
16 And ye shall be betrayed both by parents, and brethren, and kinsfolks, and friends; and [some] of you shall they cause to be put to death.
Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
17 And ye shall be hated of all [men] for my name’s sake.
Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
18 But there shall not an hair of your head perish.
Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
19 In your patience possess ye your souls.
Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
20 And when ye shall see Jerusalem compassed with armies, then know that the desolation thereof is nigh.
“In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
21 Then let them which are in Judæa flee to the mountains; and let them which are in the midst of it depart out; and let not them that are in the countries enter thereinto.
A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
22 For these be the days of vengeance, that all things which are written may be fulfilled.
Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
23 But woe unto them that are with child, and to them that give suck, in those days! for there shall be great distress in the land, and wrath upon this people.
Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
24 And they shall fall by the edge of the sword, and shall be led away captive into all nations: and Jerusalem shall be trodden down of the Gentiles, until the times of the Gentiles be fulfilled.
Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
25 And there shall be signs in the sun, and in the moon, and in the stars; and upon the earth distress of nations, with perplexity; the sea and the waves roaring;
“Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
26 Men’s hearts failing them for fear, and for looking after those things which are coming on the earth: for the powers of heaven shall be shaken.
Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
27 And then shall they see the Son of man coming in a cloud with power and great glory.
A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
28 And when these things begin to come to pass, then look up, and lift up your heads; for your redemption draweth nigh.
Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
29 And he spake to them a parable; Behold the fig tree, and all the trees;
Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
30 When they now shoot forth, ye see and know of your own selves that summer is now nigh at hand.
A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
31 So likewise ye, when ye see these things come to pass, know ye that the kingdom of God is nigh at hand.
Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
32 Verily I say unto you, This generation shall not pass away, till all be fulfilled.
“Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
33 Heaven and earth shall pass away: but my words shall not pass away.
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
34 And take heed to yourselves, lest at any time your hearts be overcharged with surfeiting, and drunkenness, and cares of this life, and [so] that day come upon you unawares.
“Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
35 For as a snare shall it come on all them that dwell on the face of the whole earth.
Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
36 Watch ye therefore, and pray always, that ye may be accounted worthy to escape all these things that shall come to pass, and to stand before the Son of man.
Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
37 And in the day time he was teaching in the temple; and at night he went out, and abode in the mount that is called [the mount] of Olives.
Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
38 And all the people came early in the morning to him in the temple, for to hear him.
Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.

< Luke 21 >