< Joshua 19 >
1 And the second lot came forth to Simeon, [even] for the tribe of the children of Simeon according to their families: and their inheritance was within the inheritance of the children of Judah.
Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
2 And they had in their inheritance Beer-sheba, or Sheba, and Moladah,
Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
3 And Hazar-shual, and Balah, and Azem,
Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
4 And Eltolad, and Bethul, and Hormah,
Eltolad, Betul, Horma,
5 And Ziklag, and Beth-marcaboth, and Hazar-susah,
Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
6 And Beth-lebaoth, and Sharuhen; thirteen cities and their villages:
Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
7 Ain, Remmon, and Ether, and Ashan; four cities and their villages:
Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
8 And all the villages that [were] round about these cities to Baalath-beer, Ramath of the south. This [is] the inheritance of the tribe of the children of Simeon according to their families.
da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
9 Out of the portion of the children of Judah [was] the inheritance of the children of Simeon: for the part of the children of Judah was too much for them: therefore the children of Simeon had their inheritance within the inheritance of them.
Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
10 And the third lot came up for the children of Zebulun according to their families: and the border of their inheritance was unto Sarid:
Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
11 And their border went up toward the sea, and Maralah, and reached to Dabbasheth, and reached to the river that [is] before Jokneam;
Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
12 And turned from Sarid eastward toward the sunrising unto the border of Chisloth-tabor, and then goeth out to Daberath, and goeth up to Japhia,
Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
13 And from thence passeth on along on the east to Gittah-hepher, to Ittah-kazin, and goeth out to Remmon-methoar to Neah;
Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
14 And the border compasseth it on the north side to Hannathon: and the outgoings thereof are in the valley of Jiphthah-el:
A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
15 And Kattath, and Nahallal, and Shimron, and Idalah, and Beth-lehem: twelve cities with their villages.
Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
16 This [is] the inheritance of the children of Zebulun according to their families, these cities with their villages.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
17 [And] the fourth lot came out to Issachar, for the children of Issachar according to their families.
Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
18 And their border was toward Jezreel, and Chesulloth, and Shunem,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
19 And Hapharaim, and Shion, and Anaharath,
Hafarayim, Anaharat,
20 And Rabbith, and Kishion, and Abez,
Rabbat, Kishiyon, Ebez,
21 And Remeth, and En-gannim, and En-haddah, and Beth-pazzez;
Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
22 And the coast reacheth to Tabor, and Shahazimah, and Beth-shemesh; and the outgoings of their border were at Jordan: sixteen cities with their villages.
Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
23 This [is] the inheritance of the tribe of the children of Issachar according to their families, the cities and their villages.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
24 And the fifth lot came out for the tribe of the children of Asher according to their families.
Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
25 And their border was Helkath, and Hali, and Beten, and Achshaph,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
26 And Alammelech, and Amad, and Misheal; and reacheth to Carmel westward, and to Shihor-libnath;
Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
27 And turneth toward the sunrising to Beth-dagon, and reacheth to Zebulun, and to the valley of Jiphthah-el toward the north side of Beth-emek, and Neiel, and goeth out to Cabul on the left hand,
Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
28 And Hebron, and Rehob, and Hammon, and Kanah, [even] unto great Zidon;
ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
29 And [then] the coast turneth to Ramah, and to the strong city Tyre; and the coast turneth to Hosah; and the outgoings thereof are at the sea from the coast to Achzib:
Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
30 Ummah also, and Aphek, and Rehob: twenty and two cities with their villages.
Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
31 This [is] the inheritance of the tribe of the children of Asher according to their families, these cities with their villages.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
32 The sixth lot came out to the children of Naphtali, [even] for the children of Naphtali according to their families.
Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
33 And their coast was from Heleph, from Allon to Zaanannim, and Adami, Nekeb, and Jabneel, unto Lakum; and the outgoings thereof were at Jordan:
Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
34 And [then] the coast turneth westward to Aznoth-tabor, and goeth out from thence to Hukkok, and reacheth to Zebulun on the south side, and reacheth to Asher on the west side, and to Judah upon Jordan toward the sunrising.
Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
35 And the fenced cities [are] Ziddim, Zer, and Hammath, Rakkath, and Chinnereth,
Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
36 And Adamah, and Ramah, and Hazor,
Adama, Rama, Hazor,
37 And Kedesh, and Edrei, and En-hazor,
Kedesh, Edireyi, En Hazor,
38 And Iron, and Migdal-el, Horem, and Beth-anath, and Beth-shemesh; nineteen cities with their villages.
Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
39 This [is] the inheritance of the tribe of the children of Naphtali according to their families, the cities and their villages.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
40 [And] the seventh lot came out for the tribe of the children of Dan according to their families.
Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
41 And the coast of their inheritance was Zorah, and Eshtaol, and Ir-shemesh,
Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
42 And Shaalabbin, and Ajalon, and Jethlah,
Shalim, Aiyalon, Itla,
43 And Elon, and Thimnathah, and Ekron,
Elon, Timna, Ekron,
44 And Eltekeh, and Gibbethon, and Baalath,
Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
45 And Jehud, and Bene-berak, and Gath-rimmon,
Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
46 And Me-jarkon, and Rakkon, with the border before Japho.
Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
47 And the coast of the children of Dan went out [too little] for them: therefore the children of Dan went up to fight against Leshem, and took it, and smote it with the edge of the sword, and possessed it, and dwelt therein, and called Leshem, Dan, after the name of Dan their father.
(Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
48 This [is] the inheritance of the tribe of the children of Dan according to their families, these cities with their villages.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
49 When they had made an end of dividing the land for inheritance by their coasts, the children of Israel gave an inheritance to Joshua the son of Nun among them:
Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
50 According to the word of the LORD they gave him the city which he asked, [even] Timnath-serah in mount Ephraim: and he built the city, and dwelt therein.
yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
51 These [are] the inheritances, which Eleazar the priest, and Joshua the son of Nun, and the heads of the fathers of the tribes of the children of Israel, divided for an inheritance by lot in Shiloh before the LORD, at the door of the tabernacle of the congregation. So they made an end of dividing the country.
Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.