< Joshua 12 >

1 Now these [are] the kings of the land, which the children of Israel smote, and possessed their land on the other side Jordan toward the rising of the sun, from the river Arnon unto mount Hermon, and all the plain on the east:
Waɗannan su ne sarakunan ƙasashen da Isra’ilawa suka ci da yaƙi, suka kuma mallaki ƙasarsu a gabashin Urdun, daga kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon haɗe da dukan gefen gabas na Araba.
2 Sihon king of the Amorites, who dwelt in Heshbon, [and] ruled from Aroer, which [is] upon the bank of the river Arnon, and from the middle of the river, and from half Gilead, even unto the river Jabbok, [which is] the border of the children of Ammon;
Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Ya yi mulki daga Arower wadda take iyakar kwarin Arnon, daga tsakiyar kwarin har zuwa, Kogin Yabbok, wanda yake iyakar Ammonawa. Wannan ya haɗa da rabin Gileyad.
3 And from the plain to the sea of Chinneroth on the east, and unto the sea of the plain, [even] the salt sea on the east, the way to Beth-jeshimoth; and from the south, under Ashdoth-pisgah:
Ya kuma yi mulki a kan gabashin Araba daga tekun Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri), zuwa Bet-Yeshimot da kuma kudu zuwa gangaren dutsen Fisga.
4 And the coast of Og king of Bashan, [which was] of the remnant of the giants, that dwelt at Ashtaroth and at Edrei,
Haka ma suka ci sashen Og sarkin Bashan, ɗaya daga cikin Refahiyawa na ƙarshe da ya yi mulki a Ashtarot da Edireyi.
5 And reigned in mount Hermon, and in Salcah, and in all Bashan, unto the border of the Geshurites and the Maachathites, and half Gilead, the border of Sihon king of Heshbon.
Mulkinsa ya taso daga Dutsen Hermon, da Saleka, da dukan Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa haɗe da rabin Gileyad, zuwa kan iyakar Heshbon ta sarki Sihon.
6 Them did Moses the servant of the LORD and the children of Israel smite: and Moses the servant of the LORD gave it [for] a possession unto the Reubenites, and the Gadites, and the half tribe of Manasseh.
Sai Musa, bawan Ubangiji da Isra’ilawa suka ci Sihon da Og da yaƙi. Musa bawan Ubangiji kuwa ya ba da ƙasarsu ga mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse.
7 And these [are] the kings of the country which Joshua and the children of Israel smote on this side Jordan on the west, from Baal-gad in the valley of Lebanon even unto the mount Halak, that goeth up to Seir; which Joshua gave unto the tribes of Israel [for] a possession according to their divisions;
Waɗannan su ne sarakuna da kuma ƙasashen da Yoshuwa da Isra’ilawa suka ci da yaƙi a yammancin Urdun, daga Ba’al-Gad a Kwarin Lebanon zuwa Dutsen Halak wanda ya miƙe zuwa Seyir. Yoshuwa ya raba ƙasarsu ta zama gādo ga Isra’ilawa bisa ga yadda aka raba su kabila-kabila.
8 In the mountains, and in the valleys, and in the plains, and in the springs, and in the wilderness, and in the south country; the Hittites, the Amorites, and the Canaanites, the Perizzites, the Hivites, and the Jebusites:
Ƙasar ta haɗa da ƙasar kan tudu, filayen arewanci, Araba, gangaren Dutse, da jejin, da kuma Negeb, wato, ƙasashen Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa, da Yebusiyawa.
9 The king of Jericho, one; the king of Ai, which [is] beside Beth-el, one;
Sarkin Yeriko, ɗaya sarkin Ai (kusa da Betel), ɗaya
10 The king of Jerusalem, one; the king of Hebron, one;
sarkin Urushalima, ɗaya sarkin Hebron, ɗaya
11 The king of Jarmuth, one; the king of Lachish, one;
sarkin Yarmut, ɗaya sarkin Lakish, ɗaya
12 The king of Eglon, one; the king of Gezer, one;
sarkin Eglon, ɗaya sarkin Gezer, ɗaya
13 The king of Debir, one; the king of Geder, one;
sarkin Debir, ɗaya sarkin Bet-Gader, ɗaya
14 The king of Hormah, one; the king of Arad, one;
sarkin Horma, ɗaya sarkin Arad, ɗaya
15 The king of Libnah, one; the king of Adullam, one;
sarkin Libna, ɗaya sarkin Adullam, ɗaya
16 The king of Makkedah, one; the king of Beth-el, one;
sarkin Makkeda, ɗaya sarkin Betel, ɗaya
17 The king of Tappuah, one; the king of Hepher, one;
sarkin Taffuwa, ɗaya sarkin Hefer, ɗaya
18 The king of Aphek, one; the king of Lasharon, one;
sarkin Afek, ɗaya sarkin Sharon, ɗaya
19 The king of Madon, one; the king of Hazor, one;
sarkin Madon, ɗaya sarkin Hazor, ɗaya
20 The king of Shimron-meron, one; the king of Achshaph, one;
sarkin Shimron Meron, ɗaya sarkin Akshaf, ɗaya
21 The king of Taanach, one; the king of Megiddo, one;
sarkin Ta’anak, ɗaya sarkin Megiddo, ɗaya
22 The king of Kedesh, one; the king of Jokneam of Carmel, one;
sarkin Kedesh, ɗaya sarkin Yokneyam a Karmel, ɗaya
23 The king of Dor in the coast of Dor, one; the king of the nations of Gilgal, one;
sarkin Dor (A Nafot Dor), ɗaya sarkin Goyim a Gilgal, ɗaya
24 The king of Tirzah, one: all the kings thirty and one.
sarki Tirza, ɗaya. Duka-duka dai sarakuna talatin da ɗaya ne.

< Joshua 12 >