< Job 25 >

1 Then answered Bildad the Shuhite, and said,
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 Dominion and fear [are] with him, he maketh peace in his high places.
“Mulki na Allah ne, dole a ji tsoronsa; yana tafiyar da kome yadda ya kamata a cikin sama.
3 Is there any number of his armies? and upon whom doth not his light arise?
Za a iya ƙirga rundunarsa? A kan wane ne ba ya haska haskensa?
4 How then can man be justified with God? or how can he be clean [that is] born of a woman?
Ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah? Ta yaya mutumin da mace ta haifa zai zama mai tsarki?
5 Behold even to the moon, and it shineth not; yea, the stars are not pure in his sight.
In har wata da taurari ba su da tsarki a idanunsa,
6 How much less man, [that is] a worm? and the son of man, [which is] a worm?
mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah!”

< Job 25 >