< Job 23 >
1 Then Job answered and said,
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 Even to day [is] my complaint bitter: my stroke is heavier than my groaning.
“Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
3 Oh that I knew where I might find him! [that] I might come [even] to his seat!
Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
4 I would order [my] cause before him, and fill my mouth with arguments.
Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
5 I would know the words [which] he would answer me, and understand what he would say unto me.
Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
6 Will he plead against me with [his] great power? No; but he would put [strength] in me.
Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
7 There the righteous might dispute with him; so should I be delivered for ever from my judge.
Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
8 Behold, I go forward, but he [is] not [there; ] and backward, but I cannot perceive him:
“Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
9 On the left hand, where he doth work, but I cannot behold [him: ] he hideth himself on the right hand, that I cannot see [him: ]
Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
10 But he knoweth the way that I take: [when] he hath tried me, I shall come forth as gold.
Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
11 My foot hath held his steps, his way have I kept, and not declined.
Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
12 Neither have I gone back from the commandment of his lips; I have esteemed the words of his mouth more than my necessary [food].
Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
13 But he [is] in one [mind], and who can turn him? and [what] his soul desireth, even [that] he doeth.
“Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
14 For he performeth [the thing that is] appointed for me: and many such [things are] with him.
Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
15 Therefore am I troubled at his presence: when I consider, I am afraid of him.
Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
16 For God maketh my heart soft, and the Almighty troubleth me:
Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
17 Because I was not cut off before the darkness, [neither] hath he covered the darkness from my face.
Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.