< Job 10 >
1 My soul is weary of my life; I will leave my complaint upon myself; I will speak in the bitterness of my soul.
“Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
2 I will say unto God, Do not condemn me; shew me wherefore thou contendest with me.
Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
3 [Is it] good unto thee that thou shouldest oppress, that thou shouldest despise the work of thine hands, and shine upon the counsel of the wicked?
Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
4 Hast thou eyes of flesh? or seest thou as man seeth?
Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
5 [Are] thy days as the days of man? [are] thy years as man’s days,
Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
6 That thou enquirest after mine iniquity, and searchest after my sin?
da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
7 Thou knowest that I am not wicked; and [there is] none that can deliver out of thine hand.
Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
8 Thine hands have made me and fashioned me together round about; yet thou dost destroy me.
“Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
9 Remember, I beseech thee, that thou hast made me as the clay; and wilt thou bring me into dust again?
Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
10 Hast thou not poured me out as milk, and curdled me like cheese?
Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
11 Thou hast clothed me with skin and flesh, and hast fenced me with bones and sinews.
Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
12 Thou hast granted me life and favour, and thy visitation hath preserved my spirit.
Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
13 And these [things] hast thou hid in thine heart: I know that this [is] with thee.
“Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
14 If I sin, then thou markest me, and thou wilt not acquit me from mine iniquity.
In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
15 If I be wicked, woe unto me; and [if] I be righteous, [yet] will I not lift up my head. [I am] full of confusion; therefore see thou mine affliction;
Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
16 For it increaseth. Thou huntest me as a fierce lion: and again thou shewest thyself marvellous upon me.
In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
17 Thou renewest thy witnesses against me, and increasest thine indignation upon me; changes and war [are] against me.
Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
18 Wherefore then hast thou brought me forth out of the womb? Oh that I had given up the ghost, and no eye had seen me!
“Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
19 I should have been as though I had not been; I should have been carried from the womb to the grave.
Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
20 [Are] not my days few? cease [then, and] let me alone, that I may take comfort a little,
’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
21 Before I go [whence] I shall not return, [even] to the land of darkness and the shadow of death;
kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
22 A land of darkness, as darkness [itself; and] of the shadow of death, without any order, and [where] the light [is] as darkness.
zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”