< Genesis 13 >

1 And Abram went up out of Egypt, he, and his wife, and all that he had, and Lot with him, into the south.
Saboda haka Abram ya haura daga Masar zuwa Negeb tare da matarsa, da dukan abin da yake da shi tare da Lot.
2 And Abram [was] very rich in cattle, in silver, and in gold.
Abram ya azurta ƙwarai da dabbobi, da azurfa, da kuma zinariya.
3 And he went on his journeys from the south even to Beth-el, unto the place where his tent had been at the beginning, between Beth-el and Hai;
Daga Negeb, ya ci gaba da tafiyarsa a wurare dabam-dabam har ya kai tsakanin Betel da Ai, a inda dā ya kafa tentinsa na fari
4 Unto the place of the altar, which he had made there at the first: and there Abram called on the name of the LORD.
da kuma inda dā ya gina bagade. A can Abram ya kira bisa sunan Ubangiji.
5 And Lot also, which went with Abram, had flocks, and herds, and tents.
Lot wanda yake tafiya tare da Abram, shi ma yana da garken shanu da tumaki da kuma tentuna.
6 And the land was not able to bear them, that they might dwell together: for their substance was great, so that they could not dwell together.
Wannan ya sa har ƙasar ba tă ishe su yayinda suke zama tare ba, saboda mallakarsu ta yi yawa har ba za su iya zama tare ba.
7 And there was a strife between the herdmen of Abram’s cattle and the herdmen of Lot’s cattle: and the Canaanite and the Perizzite dwelled then in the land.
Rikici kuma ya tashi tsakanin masu kiwon dabbobin Abram da na Lot. Mazaunan ƙasar, a lokacin kuwa Kan’aniyawa da Ferizziyawa ne.
8 And Abram said unto Lot, Let there be no strife, I pray thee, between me and thee, and between my herdmen and thy herdmen; for we [be] brethren.
Saboda haka Abram ya ce wa Lot, “Kada mu bar rikici yă shiga tsakaninmu, ko kuma tsakanin masu kiwon dabbobinka da nawa, gama mu’yan’uwa ne.
9 [Is] not the whole land before thee? separate thyself, I pray thee, from me: if [thou wilt take] the left hand, then I will go to the right; or if [thou depart] to the right hand, then I will go to the left.
Ba ga dukan ƙasar tana gabanka ba? Bari mu rabu. In ka yi hagu sai ni in yi dama. In ka yi dama, sai ni in yi hagu.”
10 And Lot lifted up his eyes, and beheld all the plain of Jordan, that it [was] well watered every where, before the LORD destroyed Sodom and Gomorrah, [even] as the garden of the LORD, like the land of Egypt, as thou comest unto Zoar.
Lot ya ɗaga idanunsa sama ya dubi kwarin Urdun, sai ya ga kwarin yana da ciyawa mai kyau ƙwarai sai ka ce lambun Ubangiji, kamar ƙasar Masar, wajajen Zowar. (Wannan fa kafin Ubangiji yă hallaka Sodom da Gomorra.)
11 Then Lot chose him all the plain of Jordan; and Lot journeyed east: and they separated themselves the one from the other.
Saboda haka sai Lot ya zaɓar wa kansa dukan kwarin Urdun, ya tashi ya nufi wajen gabas. Haka fa suka rabu da juna.
12 Abram dwelled in the land of Canaan, and Lot dwelled in the cities of the plain, and pitched [his] tent toward Sodom.
Abram ya zauna a ƙasar Kan’ana, yayinda Lot ya zauna cikin biranen kwari, ya kafa tentunansa kusa da Sodom.
13 But the men of Sodom [were] wicked and sinners before the LORD exceedingly.
Mutanen Sodom kuwa mugaye ne, sun aikata zunubi ƙwarai ga Ubangiji.
14 And the LORD said unto Abram, after that Lot was separated from him, Lift up now thine eyes, and look from the place where thou art northward, and southward, and eastward, and westward:
Bayan Lot ya rabu da Abram, sai Ubangiji ya ce wa Abram, “Ɗaga idanunka daga inda kake, ka dubi arewa da kudu, gabas da yamma.
15 For all the land which thou seest, to thee will I give it, and to thy seed for ever.
Dukan ƙasar da kake gani zan ba ka, kai da zuriyarka har abada.
16 And I will make thy seed as the dust of the earth: so that if a man can number the dust of the earth, [then] shall thy seed also be numbered.
Zan sa zuriyarka tă yi yawa kamar ƙurar ƙasa, har in wani yana iya ƙidaya ƙurar, to, za a iya ƙidaya zuriyarka.
17 Arise, walk through the land in the length of it and in the breadth of it; for I will give it unto thee.
Tafi, ka ratsa tsawo da fāɗin ƙasar, gama zan ba ka ita.”
18 Then Abram removed [his] tent, and came and dwelt in the plain of Mamre, which [is] in Hebron, and built there an altar unto the LORD.
Saboda haka Abram ya cire tentunansa, ya zo ya zauna kusa da manyan itatuwan Mamre a Hebron, inda ya gina bagade ga Ubangiji.

< Genesis 13 >