< 1 Corinthians 3 >
1 And I, brethren, could not speak unto you as unto spiritual, but as unto carnal, [even] as unto babes in Christ.
’Yan’uwa, ban iya yi muku magana kamar masu ruhaniya ba, sai dai kamar masu halin mutuntaka, jarirai cikin bin Kiristi kawai.
2 I have fed you with milk, and not with meat: for hitherto ye were not able [to bear it], neither yet now are ye able.
Na ba ku madara ba abinci mai tauri ba, domin ba ku balaga ba a lokacin. Kai, har yanzu ma, ba ku balaga ba.
3 For ye are yet carnal: for whereas [there is] among you envying, and strife, and divisions, are ye not carnal, and walk as men?
Har yanzu kuna rayuwa bisa ga halin mutuntaka. Da yake akwai kishi da faɗace-faɗace a cikinku, ba rayuwa irin ta halin mutuntaka ke nan kuke yi ba? Kuma ba rayuwa irin ta mutane ce kawai kuke yi ba?
4 For while one saith, I am of Paul; and another, I [am] of Apollos; are ye not carnal?
Gama sa’ad da wani ya ce, “Ni na Bulus ne,” wani kuma ya ce, “Ni na Afollos ne,” ba rayuwa irin ta mutane ke nan kuke yi ba?
5 Who then is Paul, and who [is] Apollos, but ministers by whom ye believed, even as the Lord gave to every man?
Shin, wane ne Afollos? Wane ne kuma Bulus? Ai, bayi ne kawai waɗanda ta wurinsu kuka gaskata, kamar yadda Ubangiji ya ba kowannensu aikinsa.
6 I have planted, Apollos watered; but God gave the increase.
Ni na shuka iri, Afollos kuma ya yi banruwa, amma Allah ne ya sa irin ya yi girma.
7 So then neither is he that planteth any thing, neither he that watereth; but God that giveth the increase.
Don haka, da wanda ya yi shuki, da wanda ya yi banruwa, ba a bakin kome suke ba, sai dai Allah kaɗai, mai sa abubuwa su yi girma.
8 Now he that planteth and he that watereth are one: and every man shall receive his own reward according to his own labour.
Mutumin da ya yi shuki, da mutumin da ya yi banruwa nufinsu ɗaya ne, kuma kowannensu zai sami lada gwargwadon aikinsa.
9 For we are labourers together with God: ye are God’s husbandry, [ye are] God’s building.
Gama mu abokan aiki ne na Allah; ku kuwa gonar ce ta Allah, ginin Allah kuma.
10 According to the grace of God which is given unto me, as a wise masterbuilder, I have laid the foundation, and another buildeth thereon. But let every man take heed how he buildeth thereupon.
Ta wurin alherin da Allah ya ba ni, na kafa tushen gini kamar ƙwararren magini, wani kuma dabam yana gini a kai. Amma kowa yă lura da yadda yake gini.
11 For other foundation can no man lay than that is laid, which is Jesus Christ.
Gama babu wanda zai iya kafa wani tushen gini dabam da wanda aka riga aka kafa, wanda yake Yesu Kiristi.
12 Now if any man build upon this foundation gold, silver, precious stones, wood, hay, stubble;
In wani ya yi gini a kan tushen ginin nan da zinariya, azurfa, duwatsu masu daraja, itace, ciyawa ko kara,
13 Every man’s work shall be made manifest: for the day shall declare it, because it shall be revealed by fire; and the fire shall try every man’s work of what sort it is.
aikin zai bayyana kansa, domin za a nuna shi a sarari a Ranar. Wuta ce za tă bayyana aikin, wutar kuwa za tă gwada ingancin aikin kowa.
14 If any man’s work abide which he hath built thereupon, he shall receive a reward.
In abin da kowane mutum ya gina ya tsaya, zai sami lada.
15 If any man’s work shall be burned, he shall suffer loss: but he himself shall be saved; yet so as by fire.
In ya ƙone, zai yi hasara, amma zai sami ceto, sai dai kamar wanda ya bi ta tsakiyar wuta ne.
16 Know ye not that ye are the temple of God, and [that] the Spirit of God dwelleth in you?
Ashe, ba ku sani ba cewa ku kanku haikalin Allah ne, Ruhun Allah kuma yana zaune a cikinku?
17 If any man defile the temple of God, him shall God destroy; for the temple of God is holy, which [temple] ye are.
Duk wanda ya ɓata haikalin Allah, Allah zai ɓata shi, don haikalin Allah mai tsarki ne, ku ne kuwa haikalin nan.
18 Let no man deceive himself. If any man among you seemeth to be wise in this world, let him become a fool, that he may be wise. (aiōn )
Kada ku ruɗi kanku. In waninku yana tsammani cewa yana da hikima, yadda duniya ta ɗauki hikima, to, sai ya mai da kansa “wawa” don yă zama mai hikima. (aiōn )
19 For the wisdom of this world is foolishness with God. For it is written, He taketh the wise in their own craftiness.
Gama hikimar duniyan nan, wauta ce a gaban Allah, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Yakan kama masu hikima a cikin makircinsu”;
20 And again, The Lord knoweth the thoughts of the wise, that they are vain.
kuma a rubuce yake cewa, “Ubangiji ya san dukan tunanin masu hikima banza ne.”
21 Therefore let no man glory in men. For all things are yours;
Saboda haka, kada wani yă yi taƙama da mutum! Gama kome naku ne,
22 Whether Paul, or Apollos, or Cephas, or the world, or life, or death, or things present, or things to come; all are yours;
ko Bulus ko Afollos ko Kefas ko duniya ko rai ko mutuwa ko abubuwa na yanzu ko na nan gaba, ai, duka naku ne,
23 And ye are Christ’s; and Christ [is] God’s.
ku kuwa na Kiristi ne, Kiristi kuma na Allah ne.