< Psalms 92 >
1 IT IS A GOOD THING TO GIVE THANKS UNTO THE LORD, AND TO SING PRAISES UNTO Your NAME, O MOST HIGH:
Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
2 To show forth your loving kindness in the morning, and your faithfulness every night,
don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
3 Upon an instrument of ten strings, and upon the psaltery; upon the harp with a solemn sound.
da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
4 For you, LORD, have made me glad through your work: I will triumph in the works of your hands.
Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
5 O LORD, how great are your works! and your thoughts are very deep.
Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
6 A brutish man knows not; neither does a fool understand this.
Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
7 When the wicked spring as the grass, and when all the workers of iniquity do flourish; it is that they shall be destroyed for ever:
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
8 But you, LORD, are most high for evermore.
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
9 For, lo, your enemies, O LORD, for, lo, your enemies shall perish; all the workers of iniquity shall be scattered.
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
10 But my horn shall you exalt like the horn of an unicorn (ox): I shall be anointed with fresh oil.
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
11 Mine eye also shall see my desire on mine enemies, and mine ears shall hear my desire of the wicked that rise up against me.
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
12 The righteous shall flourish like the palm tree: he shall grow like a cedar in Lebanon.
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
13 Those that be planted in the house of the LORD shall flourish in the courts of our God.
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
14 They shall still bring forth fruit in old age; they shall be fat and flourishing;
Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
15 To show that the LORD is upright: he is my rock, and there is no unrighteousness in him.
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”