< Psalms 66 >

1 Make a joyful noise unto God, all you lands:
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Sing forth the honour of his name: make his praise glorious.
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Say unto God, How terrible are you in your works! through the greatness of your power shall your enemies submit themselves unto you.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 All the earth shall worship you, and shall sing unto you; they shall sing to your name. (Selah)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Come and see the works of God: he is terrible in his doing toward the children of men.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 He turned the sea into dry land: they went through the flood on foot: there did we rejoice in him.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 He rules by his power for ever; his eyes behold the nations: let not the rebellious exalt themselves. (Selah)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 O bless our God, all of you people, and make the voice of his praise to be heard:
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 Which holds our soul in life, and suffers not our feet to be moved.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 For you, O God, have proved us: you have tried us, as silver is tried.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 You brought us into the net; you laid affliction upon our loins.
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 You have caused men to ride over our heads; we went through fire and through water: but you brought us out into a wealthy place.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 I will go into your house with burnt offerings: I will pay you my vows,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 Which my lips have uttered, and my mouth has spoken, when I was in trouble.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 I will offer unto you burnt sacrifices of fatlings, with the incense of rams; I will offer bullocks with goats. (Selah)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Come and hear, all you that fear God, and I will declare what he has done for my soul.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 I cried unto him with my mouth, and he was extolled with my tongue.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 If I regard iniquity in my heart, the Lord will not hear me:
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 But verily God has heard me; he has attended to the voice of my prayer.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Blessed be God, which has not turned away my prayer, nor his mercy from me.
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< Psalms 66 >