< Lamentations 3 >

1 I AM the man that has seen affliction by the rod of his wrath.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 He has led me, and brought me into darkness, but not into light.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Surely against me is he turned; he turns his hand against me all the day.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 My flesh and my skin has he made old; he has broken my bones.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 He has built against me, and compassed me with gall and travail.
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 He has set me in dark places, as they that be dead of old.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 He has hedged me about, that I cannot get out: he has made my chain heavy.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Also when I cry and shout, he shuts out my prayer.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 He has enclosed my ways with hewn stone, he has made my paths crooked.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 He was unto me as a bear lying in wait, and as a lion in secret places.
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 He has turned aside my ways, and pulled me in pieces: he has made me desolate.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 He has bent his bow, and set me as a mark for the arrow.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 He has caused the arrows of his quiver to enter into my reins.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 I was a derision to all my people; and their song all the day.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 He has filled me with bitterness, he has made me drunken with wormwood.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 He has also broken my teeth with gravel stones, he has covered me with ashes.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 And you have removed my soul far off from peace: I forgotten about prosperity.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 And I said, My strength and my hope is perished from the LORD:
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Remembering mine affliction and my misery, the wormwood and the gall.
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 My soul has them still in remembrance, and is humbled in me.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 This I recall to my mind, therefore have I hope.
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 It is of the LORD's mercies that we are not consumed, because his compassions fail not.
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 They are new every morning: great is your faithfulness.
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 The LORD is my portion, says my soul; therefore will I hope in him.
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 The LORD is good unto them that wait for him, to the soul that seeks him.
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 It is good that a man should both hope and quietly wait for the salvation of the LORD.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 It is good for a man that he bear the yoke of his youth.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 He sits alone and keeps silence, because he has borne it upon him.
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 He puts his mouth in the dust; if so be there may be hope.
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 He gives his cheek to him that strikes him: he is filled full with reproach.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 For the LORD will not cast off for ever:
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 But though he cause grief, yet will he have compassion according to the multitude of his mercies.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 For he does not afflict willingly nor grieve the children of men.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 To crush under his feet all the prisoners of the earth.
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 To turn aside the right of a man before the face of the most High,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 To subvert a man in his cause, the LORD approves not.
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Who is he that says, and it comes to pass, when the Lord commands it not?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Out of the mouth of the most High proceeds not evil and good?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Wherefore does a living man complain, a man for the punishment of his sins?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Let us search and try our ways, and return to the LORD.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Let us lift up our heart with our hands unto God in the heavens.
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 We have transgressed and have rebelled: you have not pardoned.
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 You have covered with anger, and persecuted us: you have slain, you have not pitied.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 You have covered yourself with a cloud, that our prayer should not pass through.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 You have made us as the waste and refuse in the midst of the people.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 All our enemies have opened their mouths against us.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Fear and a snare has come upon us, desolation and destruction.
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Mine eye runs down with rivers of water for the destruction of the daughter of my people.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Mine eye trickes down, and ceases not, without any intermission.
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 Till the LORD look down, and behold from heaven.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Mine eye affects mine heart because of all the daughters of my city.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Mine enemies chased me sore, like a bird, without cause.
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 They have cut off my life in the dungeon, and cast a stone upon me.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Waters flowed over mine head; then I said, I am cut off.
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 I called upon your name, O LORD, out of the low dungeon.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 You have heard my voice: hide not your ear at my breathing, at my cry.
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 You drew near in the day that I called upon you: you said, Fear not.
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 O LORD, you have pleaded the causes of my soul; you have redeemed my life.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 O LORD, you have seen my wrong: judge you my cause.
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 You have seen all their vengeance and all their imaginations against me.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 You have heard their reproach, O LORD, and all their imaginations against me;
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 The lips of those that rose up against me, and their device against me all the day.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Behold their sitting down, and their rising up; I am their music.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Render unto them a recompence, O LORD, according to the work of their hands.
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Give them sorrow of heart, your curse unto them.
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Persecute and destroy them in anger from under the heavens of the LORD.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Lamentations 3 >