< Ecclesiastes 7 >
1 A good name is better than precious ointment; and the day of death than the day of one's birth.
Suna mai kyau ya fi turare mai ƙanshi, kuma ranar mutuwa ta fi ranar haihuwa.
2 It is better to go to the house of mourning, than to go to the house of feasting: for that is the end of all men; and the living will lay it to his heart.
Gara a tafi gidan makoki da a je gidan biki, gama mutuwa ce ƙaddarar kowane mutum; ya kamata masu rai su lura da haka.
3 Sorrow is better than laughter: for by the sadness of the countenance the heart is made better.
Baƙin ciki ya fi dariya, gama baƙin ciki yakan kawo gyara.
4 The heart of the wise is in the house of mourning; but the heart of fools is in the house of delight.
Zuciyar masu hikima tana a gidan makoki, amma zuciya wawaye tana a gidan shagali.
5 It is better to hear the rebuke of the wise, than for a man to hear the song of fools.
Gara ka saurari tsawatawar mai hikima da ka saurari waƙar wawaye.
6 For as the crackling of thorns under a pot, so is the laughter of the fool: this also is vanity.
Kamar ƙarar ƙayar da take karce gindin tukunya, haka dariyar wawaye take. Wannan ma ba shi da amfani.
7 Surely oppression makes a wise man mad; and a gift destroys the heart.
Zalunci yakan mai da mutum mai hikima wawa, cin hanci kuma yakan lalace hali.
8 Better is the end of a thing than the beginning thereof: and the patient in spirit is better than the proud in spirit.
Ƙarshen abu ya fi farkonsa, haƙuri kuma ya fi girman kai.
9 Be not hasty in your spirit to be angry: for anger rests in the bosom of fools.
Kada ranka yă yi saurin tashi, gama fushi yana zama a cinyar wawaye.
10 Say not you, What is the cause that the former days were better than these? for you do not enquire wisely concerning this.
Kada ka ce, “Me ya sa kwanakin dā sun fi waɗannan?” Gama ba daidai ba ne a yi irin waɗannan tambayoyi.
11 Wisdom is good with an inheritance: and by it there is profit to them that see the sun.
Hikima, kamar gādo, abu mai kyau ne tana kuma da amfani ga waɗanda suka ga rana.
12 For wisdom is a defence, and money is a defence: but the excellency of knowledge is, that wisdom gives life to them that have it.
Hikima mafaka ce takan kāre mutum kamar yadda kuɗi suke yi. Kiyayewar da hikima takan yi wa mai ita ita ce amfanin ilimi.
13 Consider the work of God: for who can make that straight, which he has made crooked?
Ku lura da abin da Allah ya yi. Wa zai iya miƙe abin da ya tanƙware?
14 In the day of prosperity be joyful, but in the day of adversity consider: God also has set the one opposite to the other, to the end that man should find nothing after him.
Sa’ad da al’amura suke tafiya daidai, ka yi farin ciki, amma sa’ad da suka lalace, ka tuna, Allah ne ya yi wancan shi ne kuma ya yi wannan. Saboda haka, mutum ba zai san wani abu game da nan gabansa ba.
15 All things have I seen in the days of my vanity: there is a just man that perishes in his righteousness, and there is a wicked man that prolongs his life in his wickedness.
A cikin rayuwan nan ta rashin amfani nawa, na lura da waɗannan abubuwa biyu, mai adalci yana hallakawa cikin adalcinsa, mai mugunta kuma yana tsawon rai cikin muguntarsa.
16 Be not righteous over much; neither make yourself over wise: why should you destroy yourself?
Kada ka cika yin adalci, fiye da kima, kada kuma ka cika yin hikima, don me za ka hallaka kanka!
17 Be not over much wicked, neither be you foolish: why should you die before your time?
Kada ka cika yin mugunta, kada kuma ka cika yin wauta, don me za ka mutu kafin lokacinka?
18 It is good that you should take hold of this; yea, also from this withdraw not your hand: for he that fears God shall come out of them all.
Yana da kyau ka kama ɗaya ba tare da ka saki wancan ba. Mai tsoron Allah zai guji wuce gona da iri.
19 Wisdom strengthens the wise more than ten mighty men which are in the city.
Hikima takan sa mutum guda mai hikima yă yi ƙarfi fiye da masu mulki goma a cikin birni.
20 For there is not a just man upon earth, that does good, and sins not.
Babu mai adalci a duniya wanda yake yin abin da yake daidai da bai taɓa yin zunubi ba.
21 Also take no heed unto all words that are spoken; lest you hear your servant curse you:
Kada ka mai da hankali ga dukan abin da mutane suke faɗi, in ba haka ba wata rana za ka ji bayinka suna zaginka.
22 For oftentimes also your own heart knows that you yourself likewise have cursed others.
Gama kai kanka ka sani cewa sau da yawa ka zagi waɗansu.
23 All this have I proved by wisdom: I said, I will be wise; but it was far from me.
Dukan waɗannan na gwada su ta wurin hikima na kuma ce, “Na ƙudurta in zama mai hikima,” amma abin ya fi ƙarfina.
24 That which is far off, and exceeding deep, who can find it out?
Ko da me hikima take, Abin ya yi mana zurfi ƙwarai, yana da wuyar ganewa, wa zai iya gane shi?
25 I applied mine heart to know, and to search, and to seek out wisdom, and the reason of things, and to know the wickedness of folly, even of foolishness and madness:
Saboda haka na mai da hankalina ga fahimi, don in bincika in nemi hikima da yadda aka tsara abubuwa, in kuma fahimci wawancin mugunta da haukar wauta.
26 And I find more bitter than death the woman, whose heart is snares and nets, and her hands as bands: whoso pleases God shall escape from her; but the sinner shall be taken by her.
Sai na iske wani abin da ya fi mutuwa ɗaci mace wadda take tarko ne, wadda zuciyarta tarko ne wadda kuma hannuwanta sarƙa ne. Mutumin da ya gamshi Allah zai tsere mata, amma za tă kama mai zunubi.
27 Behold, this have I found, says the preacher, counting one by one, to find out the account:
Malami ya ce, “Duba, abin da na gane ke nan. “Na tara abu guda da wani, don in gane tsarin abubuwa,
28 Which yet my soul seeks, but I find not: one man among a thousand have I found; but a woman among all those have I not found.
yayinda nake cikin nema amma ban samu ba, sai na sami adali guda cikin dubu, amma ba mace mai adalci guda a cikinsu duka.
29 Lo, this only have I found, that God has made man upright; but they have sought out many inventions.
Wannan ne kaɗai abin da na gane. Allah ya yi mutum tsab amma sai muka rikitar da kanmu.”