< Psalms 88 >

1 O Yhwh God of my salvation, I have cried day and night before thee:
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Let my prayer come before thee: incline thine ear unto my cry;
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 For my soul is full of troubles: and my life draweth nigh unto the grave. (Sheol h7585)
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
4 I am counted with them that go down into the pit: I am as a man that hath no strength:
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 Free among the dead, like the slain that lie in the grave, whom thou rememberest no more: and they are cut off from thy hand.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Thou hast laid me in the lowest pit, in darkness, in the deeps.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Thy wrath lieth hard upon me, and thou hast afflicted me with all thy waves. (Selah)
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Thou hast put away mine acquaintance far from me; thou hast made me an abomination unto them: I am shut up, and I cannot come forth.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 Mine eye mourneth by reason of affliction: Yhwh, I have called daily upon thee, I have stretched out my hands unto thee.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 Wilt thou shew wonders to the dead? shall the dead arise and praise thee? (Selah)
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 Shall thy lovingkindness be declared in the grave? or thy faithfulness in destruction?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 Shall thy wonders be known in the dark? and thy righteousness in the land of forgetfulness?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 But unto thee have I cried, O Yhwh; and in the morning shall my prayer come before thee.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Yhwh, why castest thou off my soul? why hidest thou thy face from me?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 I am afflicted and ready to die from my youth up: while I suffer thy terrors I am distracted.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Thy fierce wrath goeth over me; thy terrors have cut me off.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 They came round about me daily like water; they compassed me about together.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Lover and friend hast thou put far from me, and mine acquaintance into darkness.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.

< Psalms 88 >