< Job 31 >
1 I made a covenant with mine eyes; why then should I look upon a maid?
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 For what portion of God is there from above? and what inheritance of the Almighty from on high?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 Is not destruction to the wicked? and a strange punishment to the workers of iniquity?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 Doth not he see my ways, and count all my steps?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 If I have walked with vanity, or if my foot hath hasted to deceit;
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 Let me be weighed in an even balance, that God may know mine integrity.
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 If my step hath turned out of the way, and mine heart walked after mine eyes, and if any blot hath cleaved to mine hands;
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 Then let me sow, and let another eat; yea, let my offspring be rooted out.
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 If mine heart have been deceived by a woman, or if I have laid wait at my neighbour’s door;
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 Then let my wife grind unto another, and let others bow down upon her.
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 For this is an heinous crime; yea, it is an iniquity to be punished by the judges.
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 For it is a fire that consumeth to destruction, and would root out all mine increase.
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 If I did despise the cause of my manservant or of my maidservant, when they contended with me;
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 What then shall I do when God riseth up? and when he visiteth, what shall I answer him?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 Did not he that made me in the womb make him? and did not one fashion us in the womb?
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 If I have withheld the poor from their desire, or have caused the eyes of the widow to fail;
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 Or have eaten my morsel myself alone, and the fatherless hath not eaten thereof;
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 ( For from my youth he was brought up with me, as with a father, and I have guided her from my mother’s womb; )
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 If I have seen any perish for want of clothing, or any poor without covering;
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 If his loins have not blessed me, and if he were not warmed with the fleece of my sheep;
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 If I have lifted up my hand against the fatherless, when I saw my help in the gate:
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 Then let mine arm fall from my shoulder blade, and mine arm be broken from the bone.
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 For destruction from God was a terror to me, and by reason of his highness I could not endure.
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 If I have made gold my hope, or have said to the fine gold, Thou art my confidence;
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 If I rejoiced because my wealth was great, and because mine hand had gotten much;
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 If I beheld the sun when it shined, or the moon walking in brightness;
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 And my heart hath been secretly enticed, or my mouth hath kissed my hand:
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 This also were an iniquity to be punished by the judge: for I should have denied the God that is above.
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 If I rejoiced at the destruction of him that hated me, or lifted up myself when evil found him:
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 Neither have I suffered my mouth to sin by wishing a curse to his soul.
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 If the men of my tabernacle said not, Oh that we had of his flesh! we cannot be satisfied.
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 The stranger did not lodge in the street: but I opened my doors to the traveller.
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 If I covered my transgressions as Adam, by hiding mine iniquity in my bosom:
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 Did I fear a great multitude, or did the contempt of families terrify me, that I kept silence, and went not out of the door?
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 Oh that one would hear me! behold, my desire is, that the Almighty would answer me, and that mine adversary had written a book.
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 Surely I would take it upon my shoulder, and bind it as a crown to me.
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 I would declare unto him the number of my steps; as a prince would I go near unto him.
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 If my land cry against me, or that the furrows likewise thereof complain;
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 If I have eaten the fruits thereof without money, or have caused the owners thereof to lose their life:
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 Let thistles grow instead of wheat, and cockle instead of barley. The words of Job are ended.
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.