< Psalms 30 >
1 I will extol thee, O YHWH; for thou hast lifted me up, and hast not made my foes to rejoice over me.
Zabura ce. Wata waƙa. Don keɓewar haikali. Ta Dawuda. Zan girmama ka Ya Ubangiji, gama ka tsamo ni daga zurfafa ba ka bar abokan gābana sun yi farin ciki a kaina ba.
2 O YHWH my Elohim, I cried unto thee, and thou hast healed me.
Ya Ubangiji Allahna, na yi kira gare ka don taimako ka kuwa warkar da ni.
3 O YHWH, thou hast brought up my soul from the grave: thou hast kept me alive, that I should not go down to the pit. (Sheol )
Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami. (Sheol )
4 Sing unto YHWH, O ye saints of his, and give thanks at the remembrance of his holiness.
Ku rera ga Ubangiji, ku tsarkakansa; ku yabi sunansa mai tsarki.
5 For his anger endureth but a moment; in his favour is life: weeping may endure for a night, but joy cometh in the morning.
Gama fushinsa na ɗan lokaci ne amma alherinsa har matuƙa ne; mai yiwuwa a yi kuka da dare amma farin ciki kan zo da safe.
6 And in my prosperity I said, I shall never be moved.
Sa’ad da nake lafiya, na ce, “Ba zan jijjigu ba.”
7 YHWH, by thy favour thou hast made my mountain to stand strong: thou didst hide thy face, and I was troubled.
Ya Ubangiji, sa’ad da ka yi mini alheri, ka sa katangar dutsena ya tsaya daram; amma sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai in cika da tsoro.
8 I cried to thee, O YHWH; and unto YHWH I made supplication.
A gare ka, ya Ubangiji, na yi kira; a gare ka Ubangiji na yi kukan neman jinƙai.
9 What profit is there in my blood, when I go down to the pit? Shall the dust praise thee? shall it declare thy truth?
“Wace riba ce a hallakata, a kuma gangarawa ta zuwa cikin rami? Ƙura za tă yabe ka ne? Za tă iya yin shelar amincinka?
10 Hear, O YHWH, and have mercy upon me: YHWH, be thou my helper.
Ka ji, ya Ubangiji, ka kuwa yi mini jinƙai; Ya Ubangiji, ka zama taimakona.”
11 Thou hast turned for me my mourning into dancing: thou hast put off my sackcloth, and girded me with gladness;
Ka mai da kukata ta zama rawa; ka tuɓe rigar makokina ka sa mini na farin ciki,
12 To the end that my glory may sing praise to thee, and not be silent. O YHWH my Elohim, I will give thanks unto thee for ever.
don zuciyata za tă iya rera gare ka ba kuwa za tă yi shiru ba. Ya Ubangiji Allahna, zan yi maka godiya har abada.