< Psalms 107 >

1 O give thanks unto YHWH, for he is good: for his mercy endureth for ever.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Let the redeemed of YHWH say so, whom he hath redeemed from the hand of the enemy;
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 And gathered them out of the lands, from the east, and from the west, from the north, and from the south.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 They wandered in the wilderness in a solitary way; they found no city to dwell in.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Hungry and thirsty, their soul fainted in them.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Then they cried unto YHWH in their trouble, and he delivered them out of their distresses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 And he led them forth by the right way, that they might go to a city of habitation.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Oh that men would praise YHWH for his goodness, and for his wonderful works to the children of men!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 For he satisfieth the longing soul, and filleth the hungry soul with goodness.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Such as sit in darkness and in the shadow of death, being bound in affliction and iron;
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Because they rebelled against the words of El, and despised the counsel of the Most High:
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Therefore he brought down their heart with labour; they fell down, and there was none to help.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Then they cried unto YHWH in their trouble, and he saved them out of their distresses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 He brought them out of darkness and the shadow of death, and brake their bands in sunder.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Oh that men would praise YHWH for his goodness, and for his wonderful works to the children of men!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 For he hath broken the gates of brass, and cut the bars of iron in sunder.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Fools because of their transgression, and because of their iniquities, are afflicted.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Their soul abhorreth all manner of meat; and they draw near unto the gates of death.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Then they cry unto YHWH in their trouble, and he saveth them out of their distresses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 He sent his word, and healed them, and delivered them from their destructions.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Oh that men would praise YHWH for his goodness, and for his wonderful works to the children of men!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 And let them sacrifice the sacrifices of thanksgiving, and declare his works with rejoicing.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 They that go down to the sea in ships, that do business in great waters;
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 These see the works of YHWH, and his wonders in the deep.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 For he commandeth, and raiseth the stormy wind, which lifteth up the waves thereof.
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 They mount up to the heaven, they go down again to the depths: their soul is melted because of trouble.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 They reel to and fro, and stagger like a drunken man, and are at their wits' end.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Then they cry unto YHWH in their trouble, and he bringeth them out of their distresses.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 He maketh the storm a calm, so that the waves thereof are still.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Then are they glad because they be quiet; so he bringeth them unto their desired haven.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Oh that men would praise YHWH for his goodness, and for his wonderful works to the children of men!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Let them exalt him also in the congregation of the people, and praise him in the assembly of the elders.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 He turneth rivers into a wilderness, and the watersprings into dry ground;
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 A fruitful land into barrenness, for the wickedness of them that dwell therein.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 He turneth the wilderness into a standing water, and dry ground into watersprings.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 And there he maketh the hungry to dwell, that they may prepare a city for habitation;
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 And sow the fields, and plant vineyards, which may yield fruits of increase.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 He blesseth them also, so that they are multiplied greatly; and suffereth not their cattle to decrease.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Again, they are minished and brought low through oppression, affliction, and sorrow.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 He poureth contempt upon princes, and causeth them to wander in the wilderness, where there is no way.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Yet setteth he the poor on high from affliction, and maketh him families like a flock.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 The righteous shall see it, and rejoice: and all iniquity shall stop her mouth.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Whoso is wise, and will observe these things, even they shall understand the lovingkindness of YHWH.
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Psalms 107 >