< Job 24 >

1 Why, seeing times are not hidden from the Almighty, do they that know him not see his days?
“Domin me Maɗaukaki ba zai sa ranar shari’a ba? Don me waɗanda suka san shi suke faman samun irin ranakun nan?
2 Some remove the landmarks; they violently take away flocks, and feed thereof.
Mugaye suna satar fili ta wurin matsar da duwatsun da aka yi iyaka da su; suna satar dabbobi su kuma yi kiwon su.
3 They drive away the ass of the fatherless, they take the widow's ox for a pledge.
Suna ƙwace wa marayu jakunansu suna kuma ƙwace wa gwauruwa sa don suna binta bashi.
4 They turn the needy out of the way: the poor of the earth hide themselves together.
Suna ture matalauta daga hanya suna kuma sa dole matalautan ƙasar su ɓoye.
5 Behold, as wild asses in the desert, go they forth to their work; rising betimes for a prey: the wilderness yieldeth food for them and for their children.
Kamar jakunan jeji a hamada, matalauta suna aikin neman abinci gonaki marasa amfani suna tanada abinci wa’ya’yansu.
6 They reap every one his corn in the field: and they gather the vintage of the wicked.
Suna girbi a gonakin da ba nasu ba, suna yin kala a gonar inabi ta mugaye.
7 They cause the naked to lodge without clothing, that they have no covering in the cold.
Don ba su da tufafi, sukan kwana tsirara; ba su da wani abin da zai rufe su cikin sanyi.
8 They are wet with the showers of the mountains, and embrace the rock for want of a shelter.
Sun jiƙe sharkaf da ruwan da yake kwararowa daga duwatsu, sun rungume duwatsu don rashin wurin fakewa.
9 They pluck the fatherless from the breast, and take a pledge of the poor.
Ana ƙwace jinjiri mai shan mama; ana ƙwace ɗan yaron matalauci don biyan bashi.
10 They cause him to go naked without clothing, and they take away the sheaf from the hungry;
Don ba su da tufafi suna yawo tsirara; suna dakon dammunan hatsi amma duk da haka suna cikin shan yunwa.
11 Which make oil within their walls, and tread their winepresses, and suffer thirst.
Suna matse zaitun a cikin kunyoyi suna kuma matse ruwan inabi daga’ya’yan inabi, duk da haka suna fama da ƙishi.
12 Men groan from out of the city, and the soul of the wounded crieth out: yet Eloah layeth not folly to them.
Ana jin nishin masu mutuwa daga birni, kuma rayukan waɗanda aka ji musu rauni suna kuka suna kira don taimako. Amma bai ba wani laifi ba.
13 They are of those that rebel against the light; they know not the ways thereof, nor abide in the paths thereof.
“Akwai waɗanda suke yi wa haske tawaye, waɗanda ba su san hanyoyinsa ba ko kuma ba su taɓa bin hanyoyinsa ba.
14 The murderer rising with the light killeth the poor and needy, and in the night is as a thief.
Sa’ad da hasken yini ya tafi, mai kisankai yakan tashi; yă je yă kashe matalauta da masu bukata; a cikin dare yake shigowa kamar ɓarawo.
15 The eye also of the adulterer waiteth for the twilight, saying, No eye shall see me: and disguiseth his face.
Idanun mazinaci suna jiran yamma ta yi sosai; yana tunani cewa, ‘Ba wanda zai gan ni,’ sai kuma yă ɓoye fuskarsa.
16 In the dark they dig through houses, which they had marked for themselves in the daytime: they know not the light.
Cikin duhu mutane suna fasa gidaje, amma da rana sukan kulle kansu; ba sa so wani abu yă haɗa su da haske.
17 For the morning is to them even as the shadow of death: if one know them, they are in the terrors of the shadow of death.
Gama dukansu, duhu mai yawa shi ne safiyarsu; suna abokantaka da razanar duhu.
18 He is swift as the waters; their portion is cursed in the earth: he beholdeth not the way of the vineyards.
“Duk da haka kamar abu marar nauyi suke a kan ruwa; gefen ƙasar da suke, an la’anta ta, yadda ba wanda yake zuwa gonar inabinsu.
19 Drought and heat consume the snow waters: so doth the grave those which have sinned. (Sheol h7585)
Kamar yadda zafi da fări suke shanye ƙanƙarar da ta narke, haka kabari zai ƙwace waɗanda suka yi zunubi. (Sheol h7585)
20 The womb shall forget him; the worm shall feed sweetly on him; he shall be no more remembered; and wickedness shall be broken as a tree.
Waɗanda suka haife su za su manta da su, tsutsotsi za su cinye su; ba za a sāke tunawa da mugaye ba amma an sare su kamar itace.
21 He evil entreateth the barren that beareth not: and doeth not good to the widow.
Suna cutar macen da ba ta da ɗa, suna nuna wa gwauruwa rashin alheri.
22 He draweth also the mighty with his power: he riseth up, and no man is sure of life.
Amma Allah cikin ikonsa yakan kawar da masu ƙarfi, ko da yake sun yi ƙarfi, ba su da tabbacin rayuwa.
23 Though it be given him to be in safety, whereon he resteth; yet his eyes are upon their ways.
Mai yiwuwa zai bar su su zauna cikin kwanciyar hankali, amma idanunsa suna kansu.
24 They are exalted for a little while, but are gone and brought low; they are taken out of the way as all other, and cut off as the tops of the ears of corn.
Sukan samu cin nasara na ɗan lokaci, amma kuma za su ɓace; za su fāɗi a tattara su kamar sauran; za a datse su kamar kan hatsi.
25 And if it be not so now, who will make me a liar, and make my speech nothing worth?
“In wannan ba haka ba ne, wane ne zai shaida ƙarya nake yi har yă ƙi yarda da maganata?”

< Job 24 >