< Psalms 145 >

1 I WILL extol thee, my God, O king; and I will bless thy name for ever and ever.
Zabura ce ta yabo. Ta Dawuda. Zan ɗaukaka ka, ya Allahna, Sarki; zan yabi sunanka har abada abadin.
2 Every day will I bless thee; and I will praise thy name for ever and ever.
Kowace rana zan yabe ka in kuma ɗaukaka sunanka har abada abadin.
3 Great is the Lord, and greatly to be praised; and his greatness is unsearchable.
Ubangiji da girma yake ya kuma cancanci yabo girmansa ya fi ƙarfin ganewar mutum.
4 One generation shall praise thy works to another, and shall declare thy mighty acts.
Tsara guda za tă yi maganar ayyukanka ga wata tsara; za su yi magana game da manyan ayyukanka.
5 I will speak of the glorious honour of thy majesty, and of thy wondrous works.
Za su yi zancen ɗaukakarka mai daraja, zan kuma yi tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
6 And men shall speak of the might of thy terrible acts: and I will declare thy greatness.
Za su yi magana game da ikon ayyukanka masu bantsoro, zan kuma yi shelar manyan ayyukanka.
7 They shall abundantly utter the memory of thy great goodness, and shall sing of thy righteousness.
Za su yi bikin yalwar alherinka suka kuma rera adalcinka da farin ciki.
8 The Lord is gracious, and full of compassion; slow to anger, and of great mercy.
Ubangiji mai alheri da kuma tausayi, mai jinkirin fushi cike kuma da ƙauna.
9 The Lord is good to all: and his tender mercies are over all his works.
Ubangiji nagari ne ga duka; yana tausayin dukan abubuwan da ya yi.
10 All thy works shall praise thee, O Lord; and thy saints shall bless thee.
Dukan abubuwan da ka yi za su yabe ka, ya Ubangiji; tsarkakanka za su ɗaukaka ka.
11 They shall speak of the glory of thy kingdom, and talk of thy power;
Za su yi maganar ɗaukakar mulkinka za su kuma yi zancen ikonka,
12 To make known to the sons of men his mighty acts, and the glorious majesty of his kingdom.
saboda dukan mutane su san manyan ayyukanka da ɗaukakar darajar mulkinka.
13 Thy kingdom is an everlasting kingdom, and thy dominion endureth throughout all generations.
Mulkinka madawwamin mulki ne, sarautarka kuma za tă dawwama cikin dukan zamanai. Ubangiji mai aminci ne ga dukan alkawuransa mai ƙauna kuma ga dukan abubuwan da ya yi.
14 The Lord upholdeth all that fall, and raiseth up all those that be bowed down.
Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
15 The eyes of all wait upon thee; and thou givest them their meat in due season.
Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
16 Thou openest thine hand, and satisfiest the desire of every living thing.
Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
17 The Lord is righteous in all his ways, and holy in all his works.
Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
18 The Lord is nigh unto all them that call upon him, to all that call upon him in truth.
Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
19 He will fulfil the desire of them that fear him: he also will hear their cry, and will save them.
Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
20 The Lord preserveth all them that love him: but all the wicked will he destroy.
Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
21 My mouth shall speak the praise of the Lord: and let all flesh bless his holy name for ever and ever.
Bakina zai yi magana cikin yabon Ubangiji. Bari kowace halitta ta yabi sunansa mai tsarki har abada abadin.

< Psalms 145 >