< Psalms 137 >

1 BY the rivers of Babylon, there we sat down, yea, we wept, when we remembered Zion.
A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
2 We hanged our harps upon the willows in the midst thereof.
A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
3 For there they that carried us away captive required of us a song; and they that wasted us required of us mirth, saying, Sing us one of the songs of Zion.
gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
4 How shall we sing the Lord’s song in a strange land?
Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
5 If I forget thee, O Jerusalem, let my right hand forget her cunning.
In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
6 If I do not remember thee, let my tongue cleave to the roof of my mouth; if I prefer not Jerusalem above my chief joy.
Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
7 Remember, O Lord, the children of Edom in the day of Jerusalem; who said, Rase it, rase it, even to the foundation thereof.
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
8 O daughter of Babylon, who art to be destroyed; happy shall he be, that rewardeth thee as thou hast served us.
Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
9 Happy shall he be, that taketh and dasheth thy little ones against the stones.
shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.

< Psalms 137 >