< John 6 >
1 AFTER these things Jesus went over the sea of Galilee, which is the sea of Tiberias.
Bayan waddannan abubuwa, Yesu ya ketare tekun Galili, wanda a ke kira tekun Tibariya.
2 And a great multitude followed him, because they saw his miracles which he did on them that were diseased.
Sai taro mai yawa suka bi shi domin suna ganin alamu da yake yi akan marasa lafiya.
3 And Jesus went up into a mountain, and there he sat with his disciples.
Sai Yesu ya hau dutse ya zauna a can tare da almajiransa.
4 And the passover, a feast of the Jews, was nigh.
(Kuma da idin Ketarewa, wato idin Yahudawa, ya kusato.)
5 When Jesus then lifted up his eyes, and saw a great company come unto him, he saith unto Philip, Whence shall we buy bread, that these may eat?
Da Yesu ya daga kai sai ya ga babban taro yana zuwa wurinsa, sai ya ce ma Filibus, “Ina za mu sayi gurasar da Mutanen nan za su ci?”
6 And this he said to prove him: for he himself knew what he would do.
( Ya fadi haka ne domin ya gwada shi, saboda shi kansa ya san abin da zai yi.)
7 Philip answered him, Two hundred pennyworth of bread is not sufficient for them, that every one of them may take a little.
Filibus ya amsa masa, “gurasar dinari biyu ma ba zata ishi kowannensu ya samu ko kadan ba.”
8 One of his disciples, Andrew, Simon Peter’s brother, saith unto him,
Daya daga cikin almajiransa, wato Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus, ya ce masa,
9 There is a lad here, which hath five barley loaves, and two small fishes: but what are they among so many?
“Ga wani dan yaro nan da dunkule biyar na sha'ir, da kifi biyu. Amma menene wadannan za su yi wa mutane masu yawa?”
10 And Jesus said, Make the men sit down. Now there was much grass in the place. So the men sat down, in number about five thousand.
Yesu ya ce, “ku sa mutane su zauna.”( wurin kuwa akwai ciyawa.) Sai mazajen suka zauna, sun kai wajen dubu biyar.
11 And Jesus took the loaves; and when he had given thanks, he distributed to the disciples, and the disciples to them that were set down; and likewise of the fishes as much as they would.
Sai Yesu ya dauki gurasar, bayan da ya yi godiya, sai ya rarraba wa wadanda suke zaune. Haka kuma ya rarraba kifin gwargwadon abin da zai ishe su.
12 When they were filled, he said unto his disciples, Gather up the fragments that remain, that nothing be lost.
Da Mutanen suka ci suka kuma koshi, sai ya ce wa almajiransa, ku tattara gutsattsarin da suka rage, kada ya zama asara.”
13 Therefore they gathered them together, and filled twelve baskets with the fragments of the five barley loaves, which remained over and above unto them that had eaten.
Sai suka cika kwanduna goma sha biyu da gutsattsarin gurasar nan biyar da ya rage bayan da kowa ya ci.
14 Then those men, when they had seen the miracle that Jesus did, said, This is of a truth that prophet that should come into the world.
Da jama'a suka ga alamar da ya yi, sai suka ce, “Hakika wannan shi ne annabin nan mai zuwa cikin duniya.
15 When Jesus therefore perceived that they would come and take him by force, to make him a king, he departed again into a mountain himself alone.
“Da Yesu ya gane suna shirin zuwa su dauke shi da karfi da yaji su nada shi sarki, sai ya sake komawa kan dutsen da kansa.
16 And when even was now come, his disciples went down unto the sea,
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara teku.
17 And entered into a ship, and went over the sea toward Capernaum. And it was now dark, and Jesus was not come to them.
Suka shiga cikin jirgi, suka haye teku zuwa kafarnahum. (A lokacin duhu ya yi, Yesu kuwa bai riga ya iso wurinsu ba tukuna.)
18 And the sea arose by reason of a great wind that blew.
Iska mai karfin gaske tana kadawa, kuma tekun yana hargowa.
19 So when they had rowed about five and twenty or thirty furlongs, they see Jesus walking on the sea, and drawing nigh unto the ship: and they were afraid.
Bayan da almajiran suka yi tuki na wajen kimanin mil ashirin da biyar ko talatin, sai suka hango Yesu yana tafiya a kan teku ya kuma kusa da jirgin, sai suka firgita.
20 But he saith unto them, It is I; be not afraid.
Amma ya ce masu, “Ni ne! kada ku firgita.”
21 Then they willingly received him into the ship: and immediately the ship was at the land whither they went.
Sa'an nan suka yarda suka karbe shi a cikin jirgin, kuma nan da nan jirgin ya kai gacci.
22 The day following, when the people which stood on the other side of the sea saw that there was none other boat there, save that one whereinto his disciples were entered, and that Jesus went not with his disciples into the boat, but that his disciples were gone away alone;
Kashe gari, sauran taron da suke tsaye a dayan hayin tekun suka ga cewa babu wani jirgi a wajen sai dayan, Yesu kuma bai shiga ciki da almajiransa ba, amma almajiransa suka tafi su kadai.
23 (Howbeit there came other boats from Tiberias nigh unto the place where they did eat bread, after that the Lord had given thanks: )
Sai dai, akwai wadansu jirage da suka zo daga Tibariya kusa da wurin da taron suka ci gurasa bayan da Ubangiji ya yi godiya.
24 When the people therefore saw that Jesus was not there, neither his disciples, they also took shipping, and came to Capernaum, seeking for Jesus.
Sa'anda taron suka gane cewa Yesu da almajiransa ba su wurin, su da kansu su ka shiga cikin jiragen suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
25 And when they had found him on the other side of the sea, they said unto him, Rabbi, when camest thou hither?
Da suka same shi a hayin tekun, suka ce masa, “Mallam, yaushe ka zo nan?”
26 Jesus answered them and said, Verily, verily, I say unto you, Ye seek me, not because ye saw the miracles, but because ye did eat of the loaves, and were filled.
Yesu ya amsa masu, da cewa, “hakika, kuna nema na ne, ba don kun ga alamu ba, amma domin kun ci gurasar nan kun koshi.
27 Labour not for the meat which perisheth, but for that meat which endureth unto everlasting life, which the Son of man shall give unto you: for him hath God the Father sealed. (aiōnios )
Ku daina yin wahala a kan neman abinci mai lalacewa, sai dai a kan abinci mai dawwama wanda zai kaiku ga rai madawwami wanda Dan Mutum zai ba ku, domin Ubangiji Allah ya sa hatiminsa a kansa.” (aiōnios )
28 Then said they unto him, What shall we do, that we might work the works of God?
Sai suka ce Masa, “Me za mu yi, domin mu aikata ayyukan Allah?
29 Jesus answered and said unto them, This is the work of God, that ye believe on him whom he hath sent.
Yesu ya amsa, “Wannan shi ne aikin Allah: wato ku gaskata da wanda ya aiko.”
30 They said therefore unto him, What sign shewest thou then, that we may see, and believe thee? what dost thou work?
Sai suka ce masa, “To wace alama za ka yi, don mu gani mu gaskata ka?
31 Our fathers did eat manna in the desert; as it is written, He gave them bread from heaven to eat.
Me za ka yi? Kakanninmu sun ci manna a jeji, kamar yadda aka rubuta, “Ya ba su gurasa daga sama su ci.”
32 Then Jesus said unto them, Verily, verily, I say unto you, Moses gave you not that bread from heaven; but my Father giveth you the true bread from heaven.
Sa'an nan Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, ina gaya maku ba Musa ne ya ba ku gurasa nan daga sama ba, amma Ubana ne ya baku gurasa ta gaskiya daga sama.
33 For the bread of God is he which cometh down from heaven, and giveth life unto the world.
Gurasar Allah itace mai saukowa daga sama mai kuma bada rai ga duniya,”
34 Then said they unto him, Lord, evermore give us this bread.
Sai suka ce masa, “Mallam, ka rika ba mu irin wannan gurasa kodayaushe.”
35 And Jesus said unto them, I am the bread of life: he that cometh to me shall never hunger; and he that believeth on me shall never thirst.
Yesu ya ce masu, “Ni ne gurasa mai ba da rai. Wanda ya zo wurina ba zai ji yunwa ba, wanda kuma ya gaskanta da ni ba zai kara jin kishi ba.
36 But I said unto you, That ye also have seen me, and believe not.
Amma na gaya maku cewa, hakika kun gan ni, duk da haka ba ku ba da gaskiya ba.
37 All that the Father giveth me shall come to me; and him that cometh to me I will in no wise cast out.
Duk wanda Uba ya bani zai zo gare ni, wanda kuwa ya zo gare ni ba zan kore shi ba ko kadan.
38 For I came down from heaven, not to do mine own will, but the will of him that sent me.
Gama na sauko daga sama, ba domin in bi nufin kaina ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni.
39 And this is the Father’s will which hath sent me, that of all which he hath given me I should lose nothing, but should raise it up again at the last day.
Wannan shi ne nufin wanda ya aiko ni, kada in rasa ko daya daga cikin wadannan da ya bani, sai dai in tashe su a ranar karshe.
40 And this is the will of him that sent me, that every one which seeth the Son, and believeth on him, may have everlasting life: and I will raise him up at the last day. (aiōnios )
Gama wannan shi ne nufin Ubana, duk wanda yake ganin Dan ya kuma gaskata da shi zai sami rai madawwami, ni kuma zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios )
41 The Jews then murmured at him, because he said, I am the bread which came down from heaven.
Sai Yahudawa suka yi gunaguni akansa, domin ya ce, “Nine Gurasar da ta sauko daga sama.”
42 And they said, Is not this Jesus, the son of Joseph, whose father and mother we know? how is it then that he saith, I came down from heaven?
Suka ce, “Ba wannan ne Yesu Dan Yusufu, wanda Ubansa da Uwarsa mun san su ba? Ta yaya yanzu zai ce, 'Na ya sauko daga sama'?
43 Jesus therefore answered and said unto them, Murmur not among yourselves.
Yesu ya amsa, ya ce masu, “Kada ku yi gunaguni a junanku.
44 No man can come to me, except the Father which hath sent me draw him: and I will raise him up at the last day.
Ba mai iya zuwa wurina sai dai in Uba wanda ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta karshe.
45 It is written in the prophets, And they shall be all taught of God. Every man therefore that hath heard, and hath learned of the Father, cometh unto me.
A rubuce yake cikin litattafan anabawa cewa, 'Dukkansu Allah zai koya masu'. Duk wanda ya ji ya kuma koya daga wurin Uba, ya kan zo gare ni.
46 Not that any man hath seen the Father, save he which is of God, he hath seen the Father.
Ba cewa wani ya taba ganin Uban ba, sai shi wanda yake daga wurin Allah - shine ya ga Uban.
47 Verily, verily, I say unto you, He that believeth on me hath everlasting life. (aiōnios )
Hakika, hakika, wanda ya bada gaskiya, yana da rai Madawwami. (aiōnios )
48 I am that bread of life.
Ni ne Gurasa ta rai.
49 Your fathers did eat manna in the wilderness, and are dead.
Ubanninku sun ci manna cikin jeji, suka kuma mutu.
50 This is the bread which cometh down from heaven, that a man may eat thereof, and not die.
Ga gurasa da ta sauko daga sama, domin mutum ya ci daga cikinta ba kuwa zai mutu ba.
51 I am the living bread which came down from heaven: if any man eat of this bread, he shall live for ever: and the bread that I will give is my flesh, which I will give for the life of the world. (aiōn )
Ni ne gurasa mai rai da ya sauko daga sama. Duk wanda ya ci daga gurasar, zai rayu har abada. Wannan gurasar da zan bayar jiki na ne don ceton duniya.” (aiōn )
52 The Jews therefore strove among themselves, saying, How can this man give us his flesh to eat?
Sai Yahudawa suka fusata a tsakanin junansu suka kuma fara gardama, cewa, “Yaya mutumin nan zai iya bamu naman jikinsa mu ci?
53 Then Jesus said unto them, Verily, verily, I say unto you, Except ye eat the flesh of the Son of man, and drink his blood, ye have no life in you.
Sai Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, in ba ku ci naman jikin Dan mutum ba, ba ku kuma sha jininsa ba, ba za ku sami rai a cikin ku ba.
54 Whoso eateth my flesh, and drinketh my blood, hath eternal life; and I will raise him up at the last day. (aiōnios )
Dukan wanda ya ci nama na ya kuma sha jinina yana da rai Madawwami, ni kuwa zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios )
55 For my flesh is meat indeed, and my blood is drink indeed.
Domin namana abinci ne na gaske, jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
56 He that eateth my flesh, and drinketh my blood, dwelleth in me, and I in him.
Duk wanda ya ci namana, ya kuma sha jinina yana zamne a ciki na, ni kuma a cikinsa.
57 As the living Father hath sent me, and I live by the Father: so he that eateth me, even he shall live by me.
Kamar yadda rayayyen Uba ya aiko ni, nake kuma rayuwa saboda Uban, haka ma wanda ya ci namana, zai rayu sabo da ni.
58 This is that bread which came down from heaven: not as your fathers did eat manna, and are dead: he that eateth of this bread shall live for ever. (aiōn )
Wannan itace gurasar da ta sauko daga sama, ba irin wadda Ubanninku suka ci suka mutu ba. Dukan wanda ya ci gurasar zai rayu har abada.” (aiōn )
59 These things said he in the synagogue, as he taught in Capernaum.
Yesu ya fadi wadan nan abubuwa a cikin majami'a sa'ad da yake koyarwa a Kafarnahum.
60 Many therefore of his disciples, when they had heard this, said, This is an hard saying; who can hear it?
Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan Magana yana da karfi, wa zai iya jinta?”
61 When Jesus knew in himself that his disciples murmured at it, he said unto them, Doth this offend you?
Yesu, kuwa da yake ya sani a ransa da cewa almajiransa suna gunagunin wannan, sai ya ce masu, “Wannan ya zamar maku laifi?
62 What and if ye shall see the Son of man ascend up where he was before?
Yaya Ke nan in kun ga Dan Mutum yana hawa inda yake a da?
63 It is the spirit that quickeneth; the flesh profiteth nothing: the words that I speak unto you, they are spirit, and they are life.
Ruhu shine mai bayar da rai; Jiki ba ya amfana komai. Kalmomin da na fada maku ruhu ne, da kuma rai.
64 But there are some of you that believe not. For Jesus knew from the beginning who they were that believed not, and who should betray him.
Amma fa akwai wadansun ku da ba su ba da gaskiya ba. Domin tun farko Yesu ya san wadanda ba su ba da gaskiya ba, da kuma wanda zai bashe shi.
65 And he said, Therefore said I unto you, that no man can come unto me, except it were given unto him of my Father.
Ya fada cewa, “shiyasa na gaya maku, ba mai iya zuwa wurina, sai ta wurin Uban.”
66 From that time many of his disciples went back, and walked no more with him.
Bayan haka, da yawa daga cikin almajiransa suka koma da baya, ba su kara tafiya tare da shi ba.
67 Then said Jesus unto the twelve, Will ye also go away?
Sai Yesu ya ce wa goma sha biyun, “ku ba kwa so ku tafi, ko ba haka ba?
68 Then Simon Peter answered him, Lord, to whom shall we go? thou hast the words of eternal life. (aiōnios )
Bitrus ya amsa masa ya ce, “Ya Ubangiji, gun wa za mu je? kai kake da maganar rai madawwami. (aiōnios )
69 And we believe and are sure that thou art that Christ, the Son of the living God.
Mu kwa mun gaskata mun kuma sani kai ne mai tsarkin nan na Allah.”
70 Jesus answered them, Have not I chosen you twelve, and one of you is a devil?
Yesu ya ce masu, “Ba ni na zabe ku, goma sha biyu ba, amma dayanku Iblis ne?”
71 He spake of Judas Iscariot the son of Simon: for he it was that should betray him, being one of the twelve.
Wato yana magana akan Yahuda dan Siman Iskariyoti, shi kuwa daya daga cikin sha-biyun ne, wanda zai ba da Yesu.