< Genesis 5 >

1 THIS is the book of the generations of Adam. In the day that God created man, in the likeness of God made he him;
Wannan shi ne rubutaccen tarihin zuriyar Adamu. Sa’ad da Allah ya halicci mutum, ya yi shi cikin kamannin Allah.
2 Male and female created he them; and blessed them, and called their name Adam, in the day when they were created.
Ya halicce su namiji da ta mace, ya kuma albarkace su. Sa’ad da kuma aka halicce su, ya kira su “Mutum.”
3 And Adam lived an hundred and thirty years, and begat a son in his own likeness, after his image; and called his name Seth:
Sa’ad da Adamu ya yi shekaru 130, sai ya haifi ɗa wanda ya yi kama da shi, ya kuma kira shi Set.
4 And the days of Adam after he had begotten Seth were eight hundred years: and he begat sons and daughters:
Bayan an haifi Set, Adamu ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
5 And all the days that Adam lived were nine hundred and thirty years: and he died.
Gaba ɗaya dai, Adamu ya yi shekaru 930, sa’an nan ya mutu.
6 And Seth lived an hundred and five years, and begat Enos:
Sa’ad da Set ya yi shekara 105, sai ya haifi Enosh.
7 And Seth lived after he begat Enos eight hundred and seven years, and begat sons and daughters:
Bayan ya haifi Enosh, Set ya yi shekara 807, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
8 And all the days of Seth were nine hundred and twelve years: and he died.
Gaba ɗaya dai, Set ya yi shekaru 912, sa’an nan ya mutu.
9 And Enos lived ninety years, and begat Cainan:
Sa’ad da Enosh ya yi shekara 90, sai ya haifi Kenan.
10 And Enos lived after he begat Cainan eight hundred and fifteen years, and begat sons and daughters:
Bayan ya haifi Kenan, Enosh ya yi shekara 815, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
11 And all the days of Enos were nine hundred and five years: and he died.
Gaba ɗaya dai, Enosh ya yi shekaru 905, sa’an nan ya mutu.
12 And Cainan lived seventy years, and begat Mahalaleel:
Sa’ad da Kenan ya yi shekara 70, sai ya haifi Mahalalel.
13 And Cainan lived after he begat Mahalaleel eight hundred and forty years, and begat sons and daughters:
Bayan ya haifi Mahalalel, Kenan ya yi shekara 840, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
14 And all the days of Cainan were nine hundred and ten years: and he died.
Gaba ɗaya dai, Kenan ya yi shekara 910, sa’an nan ya mutu.
15 And Mahalaleel lived sixty and five years, and begat Jared:
Sa’ad da Mahalalel ya yi shekara 65, sai ya haifi Yared.
16 And Mahalaleel lived after he begat Jared eight hundred and thirty years, and begat sons and daughters:
Bayan ya haifi Yared, Mahalalel ya yi shekara 830, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
17 And all the days of Mahalaleel were eight hundred ninety and five years: and he died.
Gaba ɗaya dai, Mahalalel ya yi shekara 895, sa’an nan ya mutu.
18 And Jared lived an hundred sixty and two years, and he begat Enoch:
Sa’ad da Yared ya yi shekara 162, sai ya haifi Enok.
19 And Jared lived after he begat Enoch eight hundred years, and begat sons and daughters:
Bayan ya haifi Enok, Yared ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
20 And all the days of Jared were nine hundred sixty and two years: and he died.
Gaba ɗaya dai, Yared ya yi shekara 962, sa’an nan ya mutu.
21 And Enoch lived sixty and five years, and begat Methuselah:
Sa’ad da Enok ya yi shekara 65, sai ya haifi Metusela.
22 And Enoch walked with God after he begat Methuselah three hundred years, and begat sons and daughters:
Bayan ya haifi Metusela, Enok ya kasance cikin zumunci da Allah shekaru 300, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
23 And all the days of Enoch were three hundred sixty and five years:
Gaba ɗaya dai, Enok ya yi shekaru 365.
24 And Enoch walked with God: and he was not; for God took him.
Enok ya kasance cikin zumunci da Allah, sa’an nan ba a ƙara ganinsa ba. Saboda Allah ya ɗauke shi.
25 And Methuselah lived an hundred eighty and seven years, and begat Lamech:
Sa’ad da Metusela ya yi shekara 187, sai ya haifi Lamek.
26 And Methuselah lived after he begat Lamech seven hundred eighty and two years, and begat sons and daughters:
Bayan ya haifi Lamek, Metusela ya yi shekaru 782, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
27 And all the days of Methuselah were nine hundred sixty and nine years: and he died.
Gaba ɗaya dai, Metusela ya yi shekaru 969, sa’an nan ya mutu.
28 And Lamech lived an hundred eighty and two years, and begat a son:
Sa’ad da Lamek ya yi shekara 182, sai ya haifi ɗa.
29 And he called his name Noah, saying, This same shall comfort us concerning our work and toil of our hands, because of the ground which the Lord hath cursed.
Ya ba shi suna Nuhu ya kuma ce, “Zai yi mana ta’aziyya a cikin aikinmu da wahalar hannuwanmu a ƙasar da Ubangiji ya la’anta.”
30 And Lamech lived after he begat Noah five hundred ninety and five years, and begat sons and daughters:
Bayan an haifi Nuhu, Lamek ya yi shekara 595, yana kuma da’ya’ya maza da mata.
31 And all the days of Lamech were seven hundred seventy and seven years: and he died.
Gaba ɗaya dai, Lamek ya yi shekaru 777, sa’an nan ya mutu.
32 And Noah was five hundred years old: and Noah begat Shem, Ham, and Japheth.
Bayan Nuhu ya yi shekara 500, sai ya haifi Shem, Ham da Yafet.

< Genesis 5 >