< Nahum 3 >
1 Woe to the bloody city! it is all full of lies and robbery; the prey departs not;
Kaiton birni mai zub da jini, wadda take cike da ƙarairayi, cike da ganima, wadda ba a rasa masu fāɗawa cikin wahala!
2 The noise of a whip, and the noise of the rattling of the wheels, and of the prancing horses, and of the jumping chariots.
Ku ji karar bulala da kwaramniyar ƙafafu, da sukuwar dawakai da girgizar kekunan yaƙi!
3 The horseman lifts up both the bright sword and the glittering spear: and there is a multitude of slain, and a great number of carcasses; and there is none end of their corpses; they stumble on their corpses:
Mahaya dawakai sun kunno kai, takuba suna walƙiya, māsu kuma suna ƙyali; ga ɗumbun da aka kashe ga tsibin matattu, gawawwaki ba iyaka, mutane suna tuntuɓe da gawawwaki,
4 Because of the multitude of the prostitutions of the well favored harlot, the mistress of witchcrafts, that sells nations through her prostitutions, and families through her witchcrafts.
duk saboda yawan sha’awace-sha’awacen karuwa, mai daɗin baki, uwargidan maita, wadda ta ɓad da al’ummai ta wurin karuwancinta ta kuma ɓad da mutane ta wurin maitancinta.
5 Behold, I am against you, says the LORD of hosts; and I will discover your skirts on your face, and I will show the nations your nakedness, and the kingdoms your shame.
“Ina gāba da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kware fatarinki a idonki. Zan nuna wa al’ummai tsiraicinki, masarautai kuma kunyarki.
6 And I will cast abominable filth on you, and make you vile, and will set you as a spectacle.
Zan watsa miki ƙazanta, in yi miki wulaƙanci in kuma mai da ke abin reni.
7 And it shall come to pass, that all they that look on you shall flee from you, and say, Nineveh is laid waste: who will bemoan her? from where shall I seek comforters for you?
Duk wanda ya gan ki zai gudu daga gare ki yana cewa, ‘Ninebe ta lalace, wa zai yi makoki domin ta?’ Ina zan sami wani wanda zai yi miki ta’aziyya?”
8 Are you better than populous No, that was situate among the rivers, that had the waters round about it, whose rampart was the sea, and her wall was from the sea?
Kin fi Tebes ne da take a bakin Nilu, da ruwa yake kewaye da ita? Rafi shi ne kāriyarta, ruwanta kuma katanga.
9 Ethiopia and Egypt were her strength, and it was infinite; Put and Lubim were your helpers.
Kush da kuma Masar su ne ƙarfinta marar iyaka; Fut da Libiya suna cikin mataimakanta.
10 Yet was she carried away, she went into captivity: her young children also were dashed in pieces at the top of all the streets: and they cast lots for her honorable men, and all her great men were bound in chains.
Duk da haka an tafi da ita ta kuma tafi bauta. Aka fyaɗa ƙanananta da ƙasa aka yayyanka su gunduwa-gunduwa a kan kowane titi. Aka jefa ƙuri’a a kan manyan mutanenta, aka daure manyan mutanenta da sarƙoƙi.
11 You also shall be drunken: you shall be hid, you also shall seek strength because of the enemy.
Ke ma za ki bugu, za ki ɓuya. Ki kuma nemi mafaka daga wurin abokin gāba.
12 All your strong holds shall be like fig trees with the first ripe figs: if they be shaken, they shall even fall into the mouth of the eater.
Dukan kagarunki suna kama da itatuwan ɓaure da’ya’yansu da suka nuna. Da an girgiza, sai ɓaure su zuba a bakin mai sha.
13 Behold, your people in the middle of you are women: the gates of your land shall be set wide open to your enemies: the fire shall devour your bars.
Dubi mayaƙanki, duk mata ne! Ƙofofin ƙasarki a buɗe suke ga abokan gābanki, wuta ta cinye madogaransu.
14 Draw you waters for the siege, fortify your strong holds: go into clay, and tread the mortar, make strong the brick kiln.
Ki ja ruwa gama za a kewaye ki da yaƙi. Ki ƙara ƙarfin kagaranki! Ki kwaɓa laka, ki sassaƙa turmi ki gyara abin yin tubali!
15 There shall the fire devour you; the sword shall cut you off, it shall eat you up like the cankerworm: make yourself many as the cankerworm, make yourself many as the locusts.
A can wuta za tă cinye ki; takobi zai sare ki, kuma kamar fāra, za a cinye ki. Ki riɓaɓɓanya kamar fāra, ki riɓaɓɓanya kamar fārin ɗango!
16 You have multiplied your merchants above the stars of heaven: the cankerworm spoils, and flees away.
Kin ƙara yawan masu kasuwancinki har sai da suka fi taurarin sama. Amma kamar fāra sun cinye ƙasar sa’an nan suka tashi, suka tafi.
17 Your crowned are as the locusts, and your captains as the great grasshoppers, which camp in the hedges in the cold day, but when the sun rises they flee away, and their place is not known where they are.
Masu tsaronki suna kama da fāri ɗango, shugabanninki sun yi cincirindo kamar fārin ɗango da suka sauka a kan bango a rana mai sanyi, amma da rana ta fito, duk za su tashi su tafi, ba kuma wanda ya san inda suka nufa.
18 Your shepherds slumber, O king of Assyria: your nobles shall dwell in the dust: your people is scattered on the mountains, and no man gathers them.
Ya sarkin Assuriya, makiyayanka sun yi barci; manyan mutanenka sun kwanta su huta. An watsar da mutanenka a cikin duwatsu, ba wanda zai tattaro su.
19 There is no healing of your bruise; your wound is grievous: all that hear the bruit of you shall clap the hands over you: for on whom has not your wickedness passed continually?
Ba abin da zai warkar da rauninka; rauninka ya yi muni. Duk wanda ya ji labarinka zai tafa hannuwansa saboda farin cikin fāɗuwarka, gama wane ne bai ji jiki a hannunka ba?