< Jonah 2 >

1 Then Jonah prayed to the LORD his God out of the fish’s belly,
Daga ciki cikin kifi, Yunana ya yi addu’a ga Ubangiji Allahnsa.
2 And said, I cried by reason of my affliction to the LORD, and he heard me; out of the belly of hell cried I, and you heard my voice. (Sheol h7585)
Ya ce, “A cikin damuwata na yi kira ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini. Daga cikin zurfi kabari na yi kiran neman taimako, ka kuwa saurari kukata. (Sheol h7585)
3 For you had cast me into the deep, in the middle of the seas; and the floods compassed me about: all your billows and your waves passed over me.
Cikin tashin hankali, ka jefa ni cikin zurfafa, a tsakiyar teku, ka kuma jujjuya ni a cikin ruwa; dukan raƙuman ruwanka da ambaliyarka sun bi ta kaina.
4 Then I said, I am cast out of your sight; yet I will look again toward your holy temple.
Sai na ce, ‘An kore ni daga fuskarka; duk da haka zan sāke duba wajen haikalinka mai tsarki.’
5 The waters compassed me about, even to the soul: the depth closed me round about, the weeds were wrapped about my head.
Ruwayen da suke kewaye da ni sun yi mini barazana, zurfi kuma ya kewaye ni, ciyayin ruwa suna nannaɗe kewaye da ni.
6 I went down to the bottoms of the mountains; the earth with her bars was about me for ever: yet have you brought up my life from corruption, O LORD my God.
Na nutsa har ƙarƙashin tuddai; a ƙarƙashin duniya, ka rufe ni har abada. Amma ka dawo da raina daga rami, Ya Ubangiji Allahna.
7 When my soul fainted within me I remembered the LORD: and my prayer came in to you, into your holy temple.
“Sa’ad da na ji raina yana rabuwa da ni, na tuna da kai ya Ubangiji, addu’ata kuma ta kai gare ka, a haikalinka mai tsarki.
8 They that observe lying vanities forsake their own mercy.
“Waɗanda suka maƙale wa gumaka marasa amfani, sukan ƙyale alherin da zai kasance nasu.
9 But I will sacrifice to you with the voice of thanksgiving; I will pay that that I have vowed. Salvation is of the LORD.
Amma ni, da waƙar godiya, zan miƙa tawa hadaya gare ka. Abin da na yi alkawari, shi ne zan yi. Ceto yakan zo ne kawai daga wurin Ubangiji.”
10 And the LORD spoke to the fish, and it vomited out Jonah on the dry land.
Sai Ubangiji ya umarci kifin, kifin kuwa ya amayar da Yunana a gaɓan teku.

< Jonah 2 >