< Job 35 >
1 Elihu spoke moreover, and said,
Sai Elihu ya ce,
2 Think you this to be right, that you said, My righteousness is more than God’s?
“Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
3 For you said, What advantage will it be to you? and, What profit shall I have, if I be cleansed from my sin?
Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
4 I will answer you, and your companions with you.
“Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
5 Look to the heavens, and see; and behold the clouds which are higher than you.
Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
6 If you sin, what do you against him? or if your transgressions be multiplied, what do you to him?
In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
7 If you be righteous, what give you him? or what receives he of your hand?
In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
8 Your wickedness may hurt a man as you are; and your righteousness may profit the son of man.
Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
9 By reason of the multitude of oppressions they make the oppressed to cry: they cry out by reason of the arm of the mighty.
“Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
10 But none says, Where is God my maker, who gives songs in the night;
Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
11 Who teaches us more than the beasts of the earth, and makes us wiser than the fowls of heaven?
wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
12 There they cry, but none gives answer, because of the pride of evil men.
Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
13 Surely God will not hear vanity, neither will the Almighty regard it.
Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
14 Although you say you shall not see him, yet judgment is before him; therefore trust you in him.
Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
15 But now, because it is not so, he has visited in his anger; yet he knows it not in great extremity:
Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
16 Therefore does Job open his mouth in vain; he multiplies words without knowledge.
Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”